< Psalms 114 >
1 When Israel came out of Egypt, the children of Jacob from a people whose language was strange to them;
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Judah became his holy place, and Israel his kingdom.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 The sea saw it, and went in flight; Jordan was turned back.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 The mountains were jumping like goats, and the little hills like lambs.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 What was wrong with you, O sea, that you went in flight? O Jordan, that you were turned back?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 You mountains, why were you jumping like goats, and you little hills like lambs?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Be troubled, O earth, before the Lord, before the God of Jacob;
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 Who made the rock into a water-spring, and the hard stone into a fountain.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.