< Psalms 103 >

1 Of David. Give praise to the Lord, O my soul; let everything in me give praise to his holy name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Give praise to the Lord, O my soul; let not all his blessings go from your memory.
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 He has forgiveness for all your sins; he takes away all your diseases;
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 He keeps back your life from destruction, crowning you with mercy and grace.
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 He makes your mouth full of good things, so that your strength is made new again like the eagle's.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 The Lord gives decisions in righteousness for all who are in trouble.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He gave knowledge of his way to Moses, and made his acts clear to the children of Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 The Lord is kind and full of pity, not quickly made angry, but ever ready to have mercy.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 His feeling will no longer be bitter; he will not keep his wrath for ever.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 He has not given us the punishment for our sins, or the reward of our wrongdoing.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as the heaven is high over the earth, so great is his mercy to his worshippers.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 As far as the east is from the west, so far has he put our sins from us.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 As a father has pity on his children, so the Lord has pity on his worshippers.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For he has knowledge of our feeble frame; he sees that we are only dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 As for man, his days are as grass: his beautiful growth is like the flower of the field.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 The wind goes over it and it is gone; and its place sees it no longer.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 But the mercy of the Lord is eternal for his worshippers, and their children's children will see his righteousness;
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 If they keep his agreement, and have his laws in mind to do them.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 The Lord has made ready his high seat in the heavens; his kingdom is ruling over all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Give praise to the Lord, you his angels, who are great in strength, doing his orders, and waiting for his voice.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Give praise to the Lord, all you his armies; and you his servants who do his pleasure.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Give praise to the Lord, all his works, in all places under his rule: give praise to the Lord, O my soul.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psalms 103 >