< Numbers 27 >
1 Then the daughters of Zelophehad, the son of Hepher, the son of Gilead, the son of Machir, the son of Manasseh, of the families of Manasseh, the son of Joseph, came forward: their names are Mahlah, Noah, and Hoglah, and Milcah, and Tirzah.
’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
2 They came before Moses and Eleazar the priest and the chiefs and all the people at the door of the Tent of meeting, and said,
Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
3 Death overtook our father in the waste land; he was not among those who were banded together with Korah against the Lord; but death came to him in his sin; and he had no sons.
“Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
4 Why is the name of our father to be taken away from among his family, because he had no son? Give us a heritage among our father's brothers.
Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
5 So Moses put their cause before the Lord.
Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
6 And the Lord said to Moses,
Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
7 What the daughters of Zelophehad say is right: certainly you are to give them a heritage among their father's brothers: and let the property which would have been their father's go to them.
“Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
8 And say to the children of Israel, If a man has no son at the time of his death, let his heritage go to his daughter.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
9 And if he has no daughter, then give his heritage to his brothers.
In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
10 And if he has no brothers, then give his heritage to his father's brothers.
In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
11 And if his father has no brothers, then give it to his nearest relation in the family, as his heritage: this is to be a decision made by law for the children of Israel, as the Lord gave orders to Moses.
In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
12 And the Lord said to Moses, Go up into this mountain of Abarim so that you may see the land which I have given to the children of Israel.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
13 And when you have seen it, you will be put to rest with your people, as your brother Aaron was:
Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
14 Because in the waste land of Zin, when the people were angry, you and he went against my word and did not keep my name holy before their eyes, at the waters. (These are the waters of Meribah in Kadesh in the waste land of Zin.)
gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
15 Then Moses said to the Lord,
Musa ya ce wa Ubangiji,
16 Let the Lord, the God of the spirits of all flesh, put a man at the head of this people,
“Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
17 To go out and come in before them and be their guide; so that the people of the Lord may not be like sheep without a keeper.
yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
18 And the Lord said to Moses, Take Joshua, the son of Nun, a man in whom is the spirit, and put your hand on him;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
19 And take him before Eleazar the priest and all the meeting of the people, and give him his orders before their eyes.
Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
20 And put your honour on him, so that all the children of Israel may be under his authority.
Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
21 He will take his place before Eleazar the priest, so that he may get directions from the Lord for him, with the Urim: at his word they will go out, and at his word they will come in, he and all the children of Israel.
Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
22 So Moses did as the Lord said: he took Joshua and put him before Eleazar the priest and the meeting of the people:
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
23 And he put his hands on him and gave him his orders, as the Lord had said by Moses.
Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.