< Numbers 1 >

1 And the Lord said to Moses in the waste land of Sinai, in the Tent of meeting, on the first day of the second month, in the second year after they came out of the land of Egypt,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Take the full number of the children of Israel, by their families, and by their fathers' houses, every male by name;
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 All those of twenty years old and over, who are able to go to war in Israel, are to be numbered by you and Aaron.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And to give you help, take one man from every tribe, the head of his father's house.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 These are the names of those who are to be your helpers: from Reuben, Elizur, the son of Shedeur;
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 From Simeon, Shelumiel, the son of Zurishaddai;
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 From Judah, Nahshon, the son of Amminadab;
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 From Issachar, Nethanel, the son of Zuar;
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 From Zebulun, Eliab, the son of Helon;
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Of the children of Joseph: from Ephraim, Elishama, the son of Ammihud; from Manasseh, Gamaliel, the son of Pedahzur,
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 From Benjamin, Abidan, the son of Gideoni;
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 From Dan, Ahiezer, the son of Ammi-shaddai;
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 From Asher, Pagiel, the son of Ochran;
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 From Gad, Eliasaph, the son of Reuel;
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 From Naphtali, Ahira, the son of Enan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These are the men named out of all the people, chiefs of their fathers' houses, heads of the tribes of Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 And Moses and Aaron took these men, marked out by name;
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And they got together all the people on the first day of the second month; and everyone made clear his family and his father's house, by the number of the names, from twenty years old and over.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 As the Lord had given orders to Moses, so they were numbered by him in the waste place of Sinai.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 The generations of the sons of Reuben, the oldest son of Israel, were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over, who was able to go to war;
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Forty-six thousand, five hundred of the tribe of Reuben were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 The generations of the sons of Simeon were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over, who was able to go to war;
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 Fifty-nine thousand, three hundred of the tribe of Simeon were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 The generations of the sons of Gad were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 Forty-five thousand, six hundred and fifty of the tribe of Gad were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 The generations of the sons of Judah were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 Seventy-four thousand, six hundred of the tribe of Judah were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 The generations of the sons of Issachar were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 Fifty-four thousand, four hundred of the tribe of Issachar were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 The generations of the sons of Zebulun were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 Fifty-seven thousand, four hundred of the tribe of Zebulun were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 The generations of the sons of Joseph were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 Forty thousand, five hundred of the tribe of Ephraim were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 The generations of the sons of Manasseh were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 Thirty-two thousand, two hundred of the tribe of Manasseh were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 The generations of the sons of Benjamin were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 Thirty-five thousand, four hundred of the tribe of Benjamin were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 The generations of the sons of Dan were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 Sixty-two thousand, seven hundred of the tribe of Dan were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 The generations of the sons of Asher were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 Forty-one thousand, five hundred of the tribe of Asher were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 The generations of the sons of Naphtali were numbered by their families and their fathers' houses, every male of twenty years old and over who was able to go to war;
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 Fifty-three thousand, four hundred of the tribe of Naphtali were numbered.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These are they who were numbered by Moses and Aaron and by the twelve chiefs of Israel, one from every tribe.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 So all those who were numbered of the children of Israel, by their families, all those of twenty years old and over who were able to go to war,
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 Were six hundred and three thousand, five hundred and fifty.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Levites, of the tribe of their fathers, were not numbered among them.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 For the Lord said to Moses,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Only the tribe of Levi is not to be numbered among the children of Israel,
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 But to them you are to give the care of the Tent of meeting with its vessels and everything in it: they are to take up the Tent, and be responsible for everything to do with it, and put up their tents round it.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 And when the Tent of meeting goes forward, the Levites are to take it down; and when it is to be put up, they are to do it: any strange person who comes near it is to be put to death.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 The children of Israel are to put up their tents, every man in his tent-circle round his flag.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But the tents of the Levites are to be round the Tent of meeting, so that wrath may not come on the children of Israel: the Tent of meeting is to be in the care of the Levites.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 So the children of Israel did as the Lord had given orders to Moses.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >