< Mark 7 >

1 And there came together to him the Pharisees and certain of the scribes who had come from Jerusalem,
Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.
2 And had seen that some of his disciples took their bread with unclean, that is, unwashed, hands.
Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba,
3 Now the Pharisees, and all the Jews, do not take food without washing their hands with care, keeping the old rule which has been handed down to them:
(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa.
4 And when they come from the market-place, they take no food till their hands are washed; and a number of other orders there are, which have been handed down to them to keep — washings of cups and pots and brass vessels.
Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
5 And the Pharisees and the scribes put the question to him, Why do your disciples not keep the rules of the fathers, but take their bread with unwashed hands?
Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, “Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?”
6 And he said, Well did Isaiah say of you, you false ones: These people give me honour with their lips, but their heart is far from me.
Amma ya amsa masu cewa, “Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni.
7 But their worship is to no purpose, while they give as their teaching the rules of men.
Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'”.
8 For, turning away from the law of God, you keep the rules of men.
Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane.
9 And he said to them, Truly you put on one side the law of God, so that you may keep the rules which have been handed down to you.
Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane.
10 For Moses said, Give honour to your father and mother, and, He who says evil of father or mother, let him have the punishment of death:
Koda shike Musa ya rubuta cewa, “ka girmama Ubanka da Uwarka”, kuma, “duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take”.
11 But you say, If a man says to his father or his mother, That by which you might have had profit from me is Corban, that is to say, Given to God,
Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, “duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)”'.
12 You no longer let him do anything for his father or his mother;
Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu.
13 Making the word of God of no effect by your rule, which you have given: and a number of other such things you do.
Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi.”
14 And turning to the people again, he said to them, Give ear to me all of you, and let my words be clear to you:
Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, “ku kasa kunne gareni, kuma ku gane.
15 There is nothing outside the man which, going into him, is able to make him unclean: but the things which come out of the man are those which make the man unclean.
Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi”
Bari mai kunnen ji, ya ji.
17 And when he had gone into the house away from all the people, his disciples put questions to him about the saying.
Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali.
18 And he said to them, Have even you so little wisdom? Do you not see that whatever goes into a man from outside is not able to make him unclean,
Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba,
19 Because it goes not into the heart but into the stomach, and goes out with the waste? He said this, making all food clean.
domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga”. Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
20 And he said, That which comes out of the man, that makes the man unclean.
Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi
21 Because from inside, from the heart of men, come evil thoughts and unclean pleasures,
Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa,
22 The taking of goods and of life, broken faith between husband and wife, the desire of wealth, wrongdoing, deceit, sins of the flesh, an evil eye, angry words, pride, foolish acts:
zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci.
23 All these evil things come from inside, and make the man unclean.
Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi.”
24 And he went away from there to the country of Tyre and Sidon. And he went into a house, desiring that no man might have knowledge of it: and he was not able to keep it secret.
Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba.
25 But a woman, whose little daughter had an unclean spirit, having had news of him, came straight away and went down at his feet.
Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa.
26 Now the woman was a Greek, a Syro-phoenician by birth: and she made a request to him that he would send the evil spirit out of her daughter.
Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
27 And he said to her, Let the children first have their food: for it is not right to take the children's bread and give it to the dogs.
Sai ya ce mata, “Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba”.
28 But she said to him in answer, Yes, Lord: even the dogs under the table take the bits dropped by the children.
Sai ta amsa masa cewa, “I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan.”
29 And he said to her, For this saying go your way; the evil spirit has gone out of your daughter.
Ya ce mata, “domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki.”
30 And she went away to her house, and saw the child on the bed, and the evil spirit gone out.
Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
31 And again he went out from Tyre, and came through Sidon to the sea of Galilee, through the country of Decapolis.
Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis.
32 And they came to him with one who had no power of hearing and had trouble in talking; and they made a request to him to put his hands on him.
Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
33 And he took him on one side from the people privately, and put his fingers into his ears, and he put water from his mouth on the man's tongue with his finger;
Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa.
34 And looking up to heaven, he took a deep breath, and said to him, Ephphatha, that is, Be open.
Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, “Ifatha”, wato, “bude!”
35 And his ears became open, and the band of his tongue was made loose, and his words became clear.
Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
36 And he gave them orders not to give news of it to anyone; but the more he made this request, so much the more they made it public.
Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina.
37 And they were overcome with wonder, saying, He has done all things well: he even gives back the power of hearing and the power of talking to those who have been without them.
kuma suna ta mamaki cewa, “Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana.”

< Mark 7 >