< Luke 9 >
1 And getting the twelve together, he gave them power and authority over all evil spirits and over diseases, to make them well.
Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
2 And he sent them out to be preachers of the kingdom of God, and to make well those who were ill.
Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 And he said to them, Take nothing for your journey, no stick or bag or bread or money, and do not take two coats.
Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
4 And if you go into a house, let that house be your resting-place till you go away.
Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
5 And if any people will not take you in, when you go away from that town, put off its dust from your feet for a witness against them.
Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
6 And they went away, journeying through all the towns, preaching the good news and making people free from diseases in all places.
Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
7 Now Herod the king had news of all these things: and he was in doubt, because it was said by some people that John had come back from the dead;
Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
8 And by some, that Elijah had come; and by others, that one of the old prophets had come back to life.
Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
9 And Herod said, I put John to death: but who is this, of whom such stories are given to me? And he had a desire to see him.
Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
10 And the twelve, when they came back, gave him an account of what they had done. And he took them with him and went away from the people to a town named Beth-saida.
Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
11 But the people, getting news of it, went after him: and he was pleased to see them, and gave them teaching about the kingdom of God, and made those well who were in need of it.
Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
12 And the day went on; and the twelve came to him and said, Send these people away so that they may go into the towns and the country round about and get resting-places and food for themselves, for we are in a waste place.
Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
13 But he said, Give them food yourselves. And they said, We have only five cakes of bread and two fishes, if we do not go and get food for all these people.
Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
14 For there were about five thousand men. And he said to his disciples, Make them be seated in groups, about fifty to a group.
Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
15 And they did so, and made them all be seated.
Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
16 And he took the five cakes of bread and the two fishes and, looking up to heaven, he said words of blessing over them, and when they had been broken, he gave them to the disciples to give to the people.
Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
17 And they all took the food and had enough; and they took up of the broken bits which were over, twelve baskets full.
Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
18 And it came about that when he was in prayer, by himself, and the disciples were with him, he put a question to them, saying, Who do the people say I am?
Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
19 And they, answering, said, John the Baptist; but others say Elijah; and others, that one of the old prophets has come back.
Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
20 And he said, But who do you say that I am? And Peter, answering, said, The Christ of God.
Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
21 But he gave them special orders, not to say this to any man;
Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
22 Saying, The Son of man will undergo much and be put on one side by the rulers and the chief priests and the teachers of the law, and be put to death, and on the third day he will come back to life.
Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
23 And he said to them all, If any man has a desire to come after me, let him give up all, and take up his cross every day, and come after me.
Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
24 For whoever has a desire to keep his life will have it taken from him, but whoever gives up his life because of me, will keep it.
Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
25 For what profit will a man have if he gets all the world, but undergoes loss or destruction himself?
Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
26 For if any man has a feeling of shame because of me or of my words, the Son of man will have shame because of him when he comes in his glory and the glory of the Father and of the holy angels.
Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
27 But truly I say to you, Some of those who are here now will have no taste of death till they see the kingdom of God.
Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
28 And about eight days after he had said these things, he took Peter and John and James with him and went up into the mountain for prayer.
Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
29 And while he was in prayer, his face was changed and his clothing became white and shining.
Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
30 And two men, Moses and Elijah, were talking with him;
Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
31 Who were seen in glory and were talking of his death which was about to take place in Jerusalem.
Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
32 Now Peter and those who were with him were overcome with sleep: but when they were fully awake, they saw his glory and the two men who were with him.
Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
33 And when they were about to go away from him, Peter said to Jesus, Master, it is good for us to be here; let us make three tents, one for you and one for Moses and one for Elijah: having no knowledge of what he was saying.
Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
34 And while he said these things, the shade of a cloud came over them, and they were full of fear when they went into the cloud.
Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
35 And there was a voice from the cloud saying, This is my Son, the man of my selection; give ear to him.
Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
36 And after the voice was gone they saw that Jesus was by himself. And they kept quiet, and said nothing at that time to anyone of the things which they had seen.
Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
37 And on the day after, when they came down from the mountain, a great band of people came to him.
Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
38 And a man from among them, crying out, said, Master, I make a request to you, give a thought to my son, for he is my only child:
Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
39 And see, a spirit takes him, and suddenly he gives a cry, twisted in pain and streaming at the lips, and when it goes away from him at last, he is marked as from blows.
Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
40 And I made a request to your disciples to send it out of him, but they were not able to do it.
Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
41 And Jesus said, O generation without faith and false in heart, how long will I have to be with you and put up with you? let your son come here.
Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
42 And while he was coming, he was pushed violently down and twisted by the evil spirit. But Jesus gave sharp orders to the unclean spirit, and made the boy well, and gave him back to his father.
Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
43 And they were full of wonder at the great power of God. But while they were all wondering at all the things which he did, he said to his disciples,
Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
44 Let these words go deep into your ears, for the Son of man will be given up into the hands of men.
“Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
45 But this saying was not clear to them and its sense was kept secret from them so that they were not able to see it: and they had fear of questioning him about it.
Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
46 Now there was a discussion among them about which of them would be the greatest.
Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
47 But when Jesus saw the reasoning of their hearts, he took a small child and put him by his side,
Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
48 And said to them, Whoever gives honour to this child in my name, gives honour to me: and whoever gives honour to me, gives honour to him who sent me: for whoever is least among you all, that man is great.
sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
49 And John, answering, said, Master, we saw a man driving out evil spirits in your name, and we did not let him do it, because he was not one of us.
Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
50 But Jesus said to him, Let him do it, for he who is not against you is for you.
Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
51 And it came about that when the days were near for him to be taken up, his face was turned to go to Jerusalem,
Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
52 And he sent men before: and they came to a small town of Samaria to make ready for him.
Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
53 But they would not have him there, because he was clearly going to Jerusalem.
Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
54 And when his disciples, James and John, saw this, they said, Lord, may we send fire from heaven and put an end to them?
Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
55 But turning round he said sharp words to them.
Amma, ya juya ya tsauta masu.
56 And they went to another small town.
Sai suka tafi wani kauye dabam.
57 And when they were on the way, a certain man said to him, I will come after you wherever you go.
Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
58 And Jesus said to him, Foxes have holes and the birds of the air have resting-places, but the Son of man has nowhere to put his head.
Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
59 And he said to another, Come after me. But he said, Lord, let me first go and give the last honours to my father.
Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
60 But he said to him, Let the dead take care of their dead; it is for you to go and give news of the kingdom of God.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
61 And another man said, I will come with you, Lord, but first let me say a last good-day to those who are at my house.
Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
62 But Jesus said, No man, having put his hand to the plough and looking back, is good enough for the kingdom of God.
Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”