< Luke 22 >

1 Now the feast of unleavened bread was near, which is called the Passover.
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 And the chief priests and the scribes were looking for a chance to put him to death, but they went in fear of the people.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 And Satan came into Judas Iscariot, who was one of the twelve.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 And he went away and had a discussion with the chief priests and the rulers, about how he might give him up to them.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 And they were glad, and undertook to give him money.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 And he made an agreement with them to give him up to them, if he got a chance, when the people were not present.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 And the day of unleavened bread came, when the Passover lamb is put to death.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 And Jesus sent Peter and John, saying, Go and make the Passover ready for us, so that we may take it.
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 And they said to him, Where are we to get it ready?
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 And he said to them, When you go into the town you will see a man coming to you with a vessel of water; go after him into the house into which he goes.
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 And say to the master of the house, The Master says, Where is the guest-room, where I may take the Passover with my disciples?
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 And he will take you up to a great room with a table and seats: there make ready.
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 And they went, and it was as he had said: and they made the Passover ready.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 And when the time had come, he took his seat, and the Apostles with him.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 And he said, I have had a great desire to keep this Passover with you before I come to my death;
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 For I say to you, I will not take it till it is made complete in the kingdom of God.
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 And he took a cup and, having given praise, he said, Make division of this among yourselves;
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 For I say to you, I will not take of the fruit of the vine till the kingdom of God has come.
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 And he took bread and, having given praise, he gave it to them when it had been broken, saying, This is my body, which is given for you: do this in memory of me.
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 And in the same way, after the meal, he took the cup, saying, This cup is the new testament, made with my blood which is given for you.
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 But the hand of him who is false to me is with me at the table.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 For it will be done to the Son of man after the purpose of God, but unhappy is that man by whom he is given up.
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 And they were wondering among themselves which of them it was who would do this thing.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 And there was an argument among them about which of them was the greatest.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 And he said, The kings of the Gentiles are lords over them, and those who have authority are given names of honour.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 But let it not be so with you; but he who is greater, let him become like the younger; and he who is chief, like a servant.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 For which is greater, the guest who is seated at a meal or the servant who is waiting on him? is it not the guest? but I am among you as a servant.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 But you are those who have kept with me through my troubles;
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 And I will give you a kingdom as my Father has given one to me,
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 So that you may take food and drink at my table in my kingdom, and be seated like kings, judging the twelve tribes of Israel.
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 Simon, Simon, Satan has made a request to have you, so that he may put you to the test as grain is tested:
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 But I have made prayer for you, that your faith may not go from you: and when you are turned again, make your brothers strong.
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 And he said to him, Lord, I am ready to go with you to prison and to death.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 And he said, I say to you, Peter, before the cock's second cry today, you will say three times that you have no knowledge of me.
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 And he said to them, When I sent you out without money or bag or shoes, were you in need of anything? And they said, Nothing.
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 And he said to them, But now, he who has a money-bag, or a bag for food, let him take it: and he who has not, let him give his coat for money and get a sword.
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 For I say to you that these words will be put into effect in me, And he was numbered among the evil-doers: for what has been said in the Writings about me has an end.
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 And they said, Lord, here are two swords. And he said, It is enough.
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 And he came out, and went, as his way was, to the Mountain of Olives, and the disciples went with him.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 And when he came to the place, he said to them, Make a prayer that you may not be put to the test.
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 And he went a little distance away from them and, falling on his knees in prayer, he said,
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 Father, if it is your pleasure, take this cup from me: but still, let your pleasure, not mine, be done.
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 And an angel from heaven came to him, to give him strength.
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 And being in great trouble of soul, the force of his prayer became stronger, and great drops, like blood, came from him, falling to the earth.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 And, getting up from prayer, he came to the disciples, and saw that they were sleeping for sorrow.
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 And he said, Why are you sleeping? Get up, and give yourselves to prayer, so that you may not be put to the test.
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 And while he was saying these words, there came a band of people, and Judas, one of the twelve, was in front of them, and he came near to Jesus to give him a kiss.
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 But Jesus said to him, Judas, will you be false to the Son of man with a kiss?
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 And when those who were with him saw what was coming, they said, Lord, may we not make use of our swords?
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 And one of them gave a blow to the servant of the high priest, cutting off his right ear.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 But Jesus, answering, said, Put up with this, at least. And touching his ear, he made it well.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 And Jesus said to the chief priests and the captains of the Temple and the rulers, who had come against him, Have you come out as against a thief, with swords and sticks?
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 When I was in the Temple with you every day, your hands were not stretched out against me: but this is your hour, and the authority of the dark power.
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 And they made him a prisoner and took him away to the house of the high priest. But Peter went after them at a distance.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 And a fire was lighted in the middle of the open square, and they were seated together, and Peter was among them.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 And a certain woman-servant, seeing him in the light of the fire, and looking at him with attention, said, This man was with him.
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But he said, Woman, it is not true; I have no knowledge of him.
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 And after a little time, another saw him and said, You are one of them; and he said, Man, I am not.
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 And after about an hour, another man said, with decision, Certainly this man was with him, for he is a Galilaean.
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 And Peter said, Man, I have no knowledge of these things of which you are talking. And straight away, while he was saying these words, there came the cry of a cock.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 And the Lord, turning, gave Peter a look. And the words of the Lord came to Peter's mind, how he had said, This night, before the hour of the cock's cry, you will be false to me three times.
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 And he went out, weeping bitterly.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 And the men in whose hands Jesus was, made sport of him and gave him blows.
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 And, covering his eyes, they said to him, Are you prophet enough to say who gave you that blow?
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 And they said a number of other evil things against him.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 And when it was day, the rulers of the people came together, with the chief priests and the scribes, and they took him before their Sanhedrin, saying,
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 If you are the Christ, say so. But he said, If I say so you will not have belief;
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 And if I put a question to you, you will not give an answer.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 But in the future the Son of man will be seated at the right hand of the power of God.
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 And they all said, Are you then the Son of God? and he said, You say that I am.
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 And they said, What more need have we of witness? we have the very words of his mouth.
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”

< Luke 22 >