< Leviticus 25 >

1 And the Lord said to Moses on Mount Sinai,
Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai ya ce,
2 Say to the children of Israel, When you come into the land which I will give you, let the land keep a Sabbath to the Lord.
“Yi wa Isra’ilawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, dole ƙasar kanta ta kiyaye Asabbaci ga Ubangiji.
3 For six years put seed into your land, and for six years give care to your vines and get in the produce of them;
Shekara shida, za ku yi shuki, shekara shida kuma za ku aske gonakin inabinku, ku kuma tattara hatsinsu.
4 But let the seventh year be a Sabbath of rest for the land, a Sabbath to the Lord; do not put seed into your land or have your vines cut.
Amma a shekara ta bakwai, ƙasar za tă sami hutun Asabbaci, Asabbaci ga Ubangiji. Kada ku yi shuki a gonakinku, ko kuwa ku aske gonakinku na inabi.
5 That which comes to growth of itself may not be cut, and the grapes of your uncared-for vines may not be taken off; let it be a year of rest for the land.
Kada ku girbe abin da ya yi girma ba tare da ku kuka shuka ba, ko ku girbe inabin da ba ku aske ba. Ƙasar za tă kasance da shekarar hutu.
6 And the Sabbath of the land will give food for you and your man-servant and your woman-servant and those working for payment, and for those of another country who are living among you;
Duk abin da gonar ta ba da amfani a shekara ta Asabbaci, zai zama abinci gare ku, wa kanku, bayinku maza da mata, da ma’aikatan da kuka ɗauka aiki, da kuma waɗanda ba zama ɗinɗinɗin suke yi tare da ku ba,
7 And for your cattle and the beasts on the land; all the natural increase of the land will be for food.
haka ma zai zama abinci domin dabbobinku, da kuma namun jeji a ƙasarku. Duk abin da ƙasar ta bayar za a ci.
8 And let seven Sabbaths of years be numbered to you, seven times seven years; even the days of seven Sabbaths of years, that is forty-nine years;
“‘Ku ƙirga asabbatai bakwai na shekaru bakwai, sau bakwai. Gama asabbatai bakwai na shekaru bakwai za su yi daidai da shekaru arba’in da tara.
9 Then let the loud horn be sounded far and wide on the tenth day of the seventh month; on the day of taking away sin let the horn be sounded through all your land.
Sa’an nan a busa ƙaho a ko’ina, a rana ta goma ga wata na bakwai; a Ranar Kafara, a busa ƙaho a dukan ƙasarku.
10 And let this fiftieth year be kept holy, and say publicly that everyone in the land is free from debt: it is the Jubilee, and every man may go back to his heritage and to his family.
Ku keɓe shekara ta hamsin ku kuma yi shelar’yanci a dukan ƙasar ga mazaunanta. Za tă zama shekarar murna gare ku; kowannenku zai koma ga mallakar iyalinsa, kuma kowa ga danginsa.
11 Let this fiftieth year be the Jubilee: no seed may be planted, and that which comes to growth of itself may not be cut, and the grapes may not be taken from the uncared-for vines.
Shekara ta hamsin za tă zama ta murna a gare ku; kada ku yi shuki, kada kuma ku yi girbi abin da ya yi girma da kansa, ko ku girbe inabin da ba ku lura da shi ba.
12 For it is the Jubilee, and it is holy to you; your food will be the natural increase of the field.
Gama shekara ce ta murna, za tă kuma zama mai tsarki a gare ku, ku dai ci abin da aka ɗauka kai tsaye daga gonaki.
13 In this year of Jubilee, let every man go back to his heritage.
“‘A wannan Shekara ta Murna, kowa zai koma ga mallakarsa.
14 And in the business of trading goods for money, do no wrong to one another.
“‘In ka sayar da gona wa wani daga mutanen ƙasarka, ko ka saya wata gona daga gare shi, kada ku cuci juna.
15 Let your exchange of goods with your neighbours have relation to the number of years after the year of Jubilee, and the number of times the earth has given her produce.
Sa’ad da mutum ya sayi fili daga abokin zamansa, kuɗin zai kasance bisa ga yawan shekara hamsin ta murna da suka wuce, da kuma bisa ga yawan shekarun noma da suka rage kafin wata shekara hamsin ta murna.
16 If the number of years is great, the price will be increased, and if the number of years is small, the price will be less, for it is the produce of a certain number of years which the man is giving you.
Idan shekarun suna da yawa, sai ku kara kuɗin filin, idan kuma shekarun ba su da yawa, sai ku rage kuɗin filin, gama ainihin abin da ake sayar maka shi ne yawan hatsin.
17 And do no wrong, one to another, but let the fear of your God be before you; for I am the Lord your God.
Kada ku cuci juna, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.
18 So keep my rules and my decisions and do them, and you will be safe in your land.
“‘Ku bi farillaina, ku kuma yi hankali ga kiyaye dokokina, za ku kuwa zauna lafiya a ƙasar.
19 And the land will give her fruit, and you will have food in full measure and be safe in the land.
Sa’an nan ƙasar za tă ba da amfaninta, za ku kuwa ci ku ƙoshi, ku kuma zauna lafiya.
20 And if you say, Where will our food come from in the seventh year, when we may not put in seed, or get in the increase
Mai yiwuwa ku ce, “Me za mu ci a shekara ta bakwai in ba mu yi shuki ko girbin hatsinmu ba?”
21 Then I will send my blessing on you in the sixth year, and the land will give fruit enough for three years.
Zan aika muku da irin albarka a shekara ta shida har da ƙasar za tă ba da amfani isashe na shekara uku.
22 And in the eighth year you will put in your seed, and get your food from the old stores, till the fruit of the ninth year is ready.
Yayinda kuke shuki a shekara ta takwas, za ku kasance da raguwa hatsi na shekarar da ta wuce, za ku kuma ci gaba da ci daga gare shi har girbin shekara ta tara yă shigo.
23 No exchange of land may be for ever, for the land is mine, and you are as my guests, living with me for a time.
“‘Kada a sayar da gona ɗinɗinɗin, gama ƙasar tawa ce, ku kuwa baƙi ne kawai, kuma’yan haya nawa.
24 Wherever there is property in land, the owner is to have the right of getting it back.
Ko’ina a ƙasar da kuke da mallaka, dole ku tanadar da dama fansar ƙasar.
25 If your brother becomes poor, and has to give up some of his land for money, his nearest relation may come and get back that which his brother has given up.
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta, ya kuma sayar da mallakarsa, sai danginsa na kusa yă je yă fanshi abin da mutumin ƙasarsa ya sayar.
26 And if he has no one to get it back for him, and later he himself gets wealth and has enough money to get it back;
In mutumin ba shi da wanda zai fansa masa ita, shi kansa kuwa ya wadace, ya kuma sami isashen halin fansarta,
27 Then let him take into account the years from the time when he gave it up, and make up the loss for the rest of the years to him who took it, and so get back his property.
sai yă lasafta yawan shekarun da aka yi tun da an sayar da filin. Kuɗin filin zai dangana ga yawan shekarun da suka rage kafin shekara hamsin ta murna da za tă zo; sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
28 But if he is not able to get it back for himself, then it will be kept by him who gave a price for it, till the year of Jubilee; and in that year it will go back to its first owner and he will have his property again.
Amma in bai sami halin sāke biyansa ba, abin nan da ya sayar zai ci gaba da zama mallakar mai sayan, sai Shekara ta Murna. Za a maido masa da ita a Shekara ta Murna, sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
29 And if a man gives his house in a walled town for money, he has the right to get it back for the space of a full year after he has given it up.
“‘In mutum ya sayar da gida a birni mai katanga, yana da izini yă fanshe shi a ƙarshen shekara guda, bayan ya sayar da shi.
30 And if he does not get it back by the end of the year, then the house in the town will become the property of him who gave the money for it, and of his children for ever; it will not go from him in the year of Jubilee.
In ba a fanshe shi a ƙarshen shekara ba, gidan da yake a birni mai katanga, zai zama mallakar na ɗinɗinɗin na mai sayan da kuma zuriyarsa. Ba za a mai da shi a Shekara ta Murna ba.
31 But houses in small unwalled towns will be the same as property in the country; they may be got back, and they will go back to their owners in the year of Jubilee.
Amma za a ɗauki gidaje a ƙauyuka marasa katanga kewaye da su daidai da gonaki. Za a iya fanshe su, a kuma mayar da su a Shekara ta Murna.
32 But the houses in the towns of the Levites may be got back by the Levites at any time.
“‘Kullum, Lawiyawa suna da izini su fanshi gidajensu a biranen Lawiyawa waɗanda suka mallaka.
33 And if a Levite does not give money to get back his property, his house in the town which was exchanged for money will come back to him in the year of Jubilee. For the houses of the towns of the Levites are their property among the children of Israel.
Saboda haka ana iya fansa mallakar Lawiyawa, wato, gidan da aka sayar a duk birnin da yake nasu, za a kuma mayar a Shekara ta Murna, gama gidaje a biranen Lawiyawa, mallakar Isra’ilawa ne.
34 But the land on the outskirts of their towns may not be exchanged for money, for it is their property for ever.
Amma kada a sayar da filayen kiwo na waɗannan birane; mallakarsu ce, ta ɗinɗinɗin.
35 And if your brother becomes poor and is not able to make a living, then you are to keep him with you, helping him as you would a man from another country who is living among you.
“‘In ɗaya daga ciki mutanen ƙasarku ya talauta, ba ya kuma iya tallafa wa kansa a cikinku, sai ku taimake shi kamar yadda za ku yi da baƙo a cikinku.
36 Take no interest from him, in money or in goods, but have the fear of your God before you, and let your brother make a living among you.
Kada ku karɓi riba ta kowace iri daga gare shi, amma ku ji tsoron Allahnku, saboda mutumin ƙasarku yă ci gaba da zama a cikinku.
37 Do not take interest on the money which you let him have or on the food which you give him.
Kada ku ba shi rancen kuɗi da ruwa, ko ku sayar masa abinci don samun riba.
38 I am the Lord your God, who took you out of the land of Egypt to give you the land of Canaan, that I might be your God.
Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, don in ba ku ƙasar Kan’ana in kuma zama Allahnku.
39 And if your brother becomes poor and gives himself to you for money, do not make use of him like a servant who is your property;
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta a cikinku, ya kuma sayar da kansa gare ku, kada ku sa yă yi kamar bawa.
40 But let him be with you as a servant working for payment, till the year of Jubilee;
Amma a ɗauke shi a matsayin ma’aikacin da aka ɗauka aiki, ko mazaunan da ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, sai yă yi muku aiki sai Shekara ta Murna.
41 Then he will go out from you, he and his children with him, and go back to his family and to the property of his fathers.
Sa’an nan a sake shi da’ya’yansa, yă kuma koma ga danginsa da mallakar kakanninsa.
42 For they are my servants whom I took out from the land of Egypt; they may not become the property of another.
Gama Isra’ilawa bayina ne, waɗanda na saya daga Masar, kada a sayar da su a matsayin bayi.
43 Do not be a hard master to him, but have the fear of God before you.
Kada ku gwada musu azaba, amma ku ji tsoron Allahnku.
44 But you may get servants as property from among the nations round about; from them you may take men-servants and women-servants.
“‘Bayinku maza da mata, za su zo daga al’ummai da suke kewaye da ku, daga gare su za ku iya saya bayi.
45 And in addition, you may get, for money, servants from among the children of other nations who are living with you, and from their families which have come to birth in your land; and these will be your property.
Za ku iya saya waɗansu mutanen da ba sa zama ɗinɗinɗin a cikinku, da kuma membobin danginsu da aka haifa a ƙasarku.
46 And they will be your children's heritage after you, to keep as their property; they will be your servants for ever; but you may not be hard masters to your countrymen, the children of Israel.
Za ku iya ba da su ga’ya’yanku a matsayin kayan gādo, za ku kuma iya mai da su bayi dukan rayuwarsu, amma kada ku yi mulki a bisa’yan’uwanku Isra’ilawa da tsanani.
47 And if one from another nation living among you gets wealth, and your countryman, at his side, becomes poor and gives himself for money to the man from another nation or to one of his family;
“‘In baƙo, ko wani da yake zama ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, ya wadace, ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku kuwa ya talauta, ya kuma sayar da kansa ga baƙon da yake zama a cikinku, ko memba na dangin baƙon,
48 After he has given himself he has the right to be made free, for a price, by one of his brothers,
yana da izini samun fansa, bayan ya sayar da kansa. Ɗaya daga cikin danginsa zai iya fansarsa.
49 Or his father's brother, or the son of his father's brother, or any near relation; or if he gets money, he may make himself free.
Kawu ko yaron ɗan’uwan mahaifin wannan mutum, ko kuwa wani dangi a cikin zuriyarsa, zai iya fanshe shi. Ko kuma in ya azurta, zai iya fansar kansa.
50 And let the years be numbered from the time when he gave himself to his owner till the year of Jubilee, and the price given for him will be in relation to the number of years, on the scale of the payment of a servant.
Da shi da mai sayansa, za su ƙirga lokaci daga shekarar da ya sayar da kansa har zuwa Shekara ta Murna. Farashin sakinsa zai dangana a kuɗin da ake biyan ma’aikacin da aka ɗauka aiki, na yawan shekarun ne.
51 If there is still a long time, he will give back, on account of it, a part of the price which was given for him.
In shekaru sun ragu, dole yă biya don fansarsa da kuɗi mai yawa fiye da wanda aka saye shi.
52 And if there is only a short time, he will take account of it with his master, and in relation to the number of years he will give back the price of making him free.
In shekarun sun rage kaɗan ne kafin Shekara ta Murna, sai yă yi lissafin wannan, yă kuma biya fansarsa daidai wa daida.
53 And he will be with him as a servant working for payment year by year; his master is not to be cruel to him before your eyes.
Sai a yi da shi kamar ma’aikacin da aka ɗauka aiki, daga shekara zuwa shekara; dole ku tabbata mai shi bai mallake shi da tsanani ba.
54 And if he is not made free in this way, he will go out in the year of Jubilee, he and his children with him.
“‘Ko ma ba a fanshe shi a ɗaya daga cikin waɗannan hanyoyi ba, sai a sake shi da’ya’yansa a Shekara ta Murna,
55 For the children of Israel are servants to me; they are my servants whom I took out of the land of Egypt: I am the Lord your God.
gama Isra’ilawa nawa ne a matsayin bayi. Su bayina ne waɗanda na saya daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.

< Leviticus 25 >