< Joshua 9 >

1 Now on hearing the news of these things, all the kings on the west side of Jordan, in the hill-country and the lowlands and by the Great Sea in front of Lebanon, the Hittites and the Amorites, the Canaanites, the Perizzites, the Hivites, and the Jebusites,
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 Came together with one purpose, to make war against Joshua and Israel.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 And the men of Gibeon, hearing what Joshua had done to Jericho and Ai,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 Acting with deceit, got food together as if for a long journey; and took old food-bags for their asses, and old and cracked wine-skins kept together with cord;
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 And put old stitched-up shoes on their feet, and old clothing on their backs; and all the food they had with them was dry and broken up.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 And they came to Joshua to the tent-circle at Gilgal, and said to him and to the men of Israel, We have come from a far country: so now make an agreement with us.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 And the men of Israel said to the Hivites, It may be that you are living among us; how then may we make an agreement with you?
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 And they said to Joshua, We are your servants. Then Joshua said to them, Who are you and where do you come from?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 And they said to him, Your servants have come from a very far country, because of the name of the Lord your God: for the story of his great name, and of all he did in Egypt has come to our ears,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 And what he did to the two kings of the Amorites east of Jordan, to Sihon, king of Heshbon, and to Og, king of Bashan, at Ashtaroth.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 So the responsible men and all the people of our country said to us, Take food with you for the journey and go to them, and say to them, We are your servants: so now make an agreement with us.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 This bread which we have with us for our food, we took warm and new from our houses when starting on our journey to you; but now see, it has become dry and broken up.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 And these wine-skins were new when we put the wine in them, and now they are cracked as you see; and our clothing and our shoes have become old because of our very long journey here.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 And the men took some of their food, without requesting directions from the Lord.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 So Joshua made peace with them, and made an agreement with them that they were not to be put to death: and the chiefs of the people took an oath to them.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Now three days after, when they had made this agreement with them, they had word that these men were their neighbours, living near them.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 And the children of Israel went forward on their journey, and on the third day came to their towns. Now their towns were Gibeon and Chephirah and Beeroth and Kiriath-jearim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 And the children of Israel did not put them to death, because the chiefs of the people had taken an oath to them by the Lord, the God of Israel. And all the people made an outcry against the chiefs.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 But all the chiefs said to the people, We have taken an oath to them by the Lord, the God of Israel, and so we may not put our hands on them.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 This is what we will do to them: we will not put them to death, for fear that wrath may come on us because of our oath to them.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 Keep them living, and let them be servants, cutting wood and getting water for all the people. And all the people did as the chiefs had said to them.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Then Joshua sent for them, and said to them, Why have you been false to us, saying, We are very far from you, when you are living among us?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Now because of this you are cursed, and you will for ever be our servants, cutting wood and getting water for the house of my God.
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 And, answering Joshua, they said, Because it came to the ears of your servants that the Lord your God had given orders to his servant Moses to give you all this land, and to send destruction on all the people living in it, because of you; so, fearing greatly for our lives because of you, we have done this.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 And now we are in your hands: do to us whatever seems good and right to you.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 So he kept them safe from the children of Israel, and did not let them be put to death.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 And that day Joshua made them servants, cutting wood and getting water for the people and for the altar of the Lord, in the place marked out by him, to this day.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Joshua 9 >