< Jonah 3 >

1 And the word of the Lord came to Jonah a second time, saying,
Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
2 Up! go to Nineveh, that great town, and give it the word which I have given you.
“Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
3 So Jonah got up and went to Nineveh as the Lord had said. Now Nineveh was a very great town, three days' journey from end to end.
Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
4 And Jonah first of all went a day's journey into the town, and crying out said, In forty days destruction will overtake Nineveh.
A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
5 And the people of Nineveh had belief in God; and a time was fixed for going without food, and they put on haircloth, from the greatest to the least.
Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
6 And the word came to the king of Nineveh, and he got up from his seat of authority, and took off his robe, and covering himself with haircloth, took his seat in the dust.
Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
7 And he had it given out in Nineveh, By the order of the king and his great men, no man or beast, herd or flock, is to have a taste of anything; let them have no food or water:
Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
8 And let man and beast be covered with haircloth, and let them make strong prayers to God: and let everyone be turned from his evil way and the violent acts of their hands.
Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
9 Who may say that God will not be turned, changing his purpose and turning away from his burning wrath, so that destruction may not overtake us?
Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
10 And God saw what they did, how they were turned from their evil way; and God's purpose was changed as to the evil which he said he would do to them, and he did it not.
Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.

< Jonah 3 >