< Job 6 >
1 And Job made answer and said,
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 If only my passion might be measured, and put into the scales against my trouble!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 For then its weight would be more than the sand of the seas: because of this my words have been uncontrolled.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For the arrows of the Ruler of all are present with me, and their poison goes deep into my spirit: his army of fears is put in order against me.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Does the ass of the fields give out his voice when he has grass? or does the ox make sounds over his food?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Will a man take food which has no taste without salt? or is there any taste in the soft substance of purslain?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 My soul has no desire for such things, they are as disease in my food.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 If only I might have an answer to my prayer, and God would give me my desire!
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 If only he would be pleased to put an end to me; and would let loose his hand, so that I might be cut off!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 So I would still have comfort, and I would have joy in the pains of death, for I have not been false to the words of the Holy One.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Have I strength to go on waiting, or have I any end to be looking forward to?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Is my strength the strength of stones, or is my flesh brass?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 I have no help in myself, and wisdom is completely gone from me.
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 He whose heart is shut against his friend has given up the fear of the Ruler of all.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 My friends have been false like a stream, like streams in the valleys which come to an end:
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Which are dark because of the ice, and the snow falling into them;
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Under the burning sun they are cut off, and come to nothing because of the heat.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 The camel-trains go out of their way; they go up into the waste and come to destruction.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 The camel-trains of Tema were searching with care, the bands of Sheba were waiting for them:
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 They were put to shame because of their hope; they came and their hope was gone.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 So have you now become to me; you see my sad condition and are in fear.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Did I say, Give me something? or, Make a payment for me out of your wealth?
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Or, Get me out of the power of my hater? or, Give money so that I may be free from the power of the cruel ones?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Give me teaching and I will be quiet; and make me see my error.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 How pleasing are upright words! but what force is there in your arguments?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 My words may seem wrong to you, but the words of him who has no hope are for the wind.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Truly, you are such as would give up the child of a dead man to his creditors, and would make a profit out of your friend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Now then, let your eyes be turned to me, for truly I will not say what is false to your face.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Let your minds be changed, and do not have an evil opinion of me; yes, be changed, for my righteousness is still in me.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Is there evil in my tongue? is not the cause of my trouble clear to me?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?