< Job 39 >
1 Have you knowledge of the rock-goats? or do you see the roes giving birth to their young?
“Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
2 Is the number of their months fixed by you? or is the time when they give birth ordered by you?
Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
3 They are bent down, they give birth to their young, they let loose the fruit of their body.
Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
4 Their young ones are strong, living in the open country; they go out and do not come back again.
’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
5 Who has let the ass of the fields go free? or made loose the bands of the loud-voiced beast?
“Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
6 To whom I have given the waste land for a heritage, and the salt land as a living-place.
Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
7 He makes sport of the noise of the town; the voice of the driver does not come to his ears;
Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
8 He goes looking for his grass-lands in the mountains, searching out every green thing.
Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
9 Will the ox of the mountains be your servant? or is his night's resting-place by your food-store?
“Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
10 Will he be pulling your plough with cords, turning up the valleys after you?
Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
11 Will you put your faith in him, because his strength is great? will you give the fruit of your work into his care?
Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
12 Will you be looking for him to come back, and get in your seed to the crushing-floor?
Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
13 Is the wing of the ostrich feeble, or is it because she has no feathers,
“Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
14 That she puts her eggs on the earth, warming them in the dust,
Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
15 Without a thought that they may be crushed by the foot, and broken by the beasts of the field?
ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
16 She is cruel to her young ones, as if they were not hers; her work is to no purpose; she has no fear.
Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
17 For God has taken wisdom from her mind, and given her no measure of knowledge.
Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
18 When she is shaking her wings on high, she makes sport of the horse and of him who is seated on him.
Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
19 Do you give strength to the horse? is it by your hand that his neck is clothed with power?
“Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
20 Is it through you that he is shaking like a locust, in the pride of his loud-sounding breath?
Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
21 He is stamping with joy in the valley; he makes sport of fear.
Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
22 In his strength he goes out against the arms of war, turning not away from the sword.
Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
23 The bow is sounding against him; he sees the shining point of spear and arrow.
Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
24 Shaking with passion, he is biting the earth; he is not able to keep quiet at the sound of the horn;
Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
25 When it comes to his ears he says, Aha! He is smelling the fight from far off, and hearing the thunder of the captains, and the war-cries.
Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
26 Is it through your knowledge that the hawk takes his flight, stretching out his wings to the south?
“Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
27 Or is it by your orders that the eagle goes up, and makes his resting-place on high?
Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
28 On the rock is his house, and on the mountain-top his strong place.
Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
29 From there he is watching for food; his eye sees it far off.
Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
30 His young have blood for their drink, and where the dead bodies are, there is he to be seen.
’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”