< Job 34 >

1 And Elihu made answer and said,
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Give ear, you wise, to my words; and you who have knowledge, give attention to me;
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 For words are tested by the ear, as food is tasted by the mouth.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Let us make the decision for ourselves as to what is right; let us have the knowledge among ourselves of what is good.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For Job has said, I am upright, and it is God who has taken away my right;
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Though I am right, still I am in pain; my wound may not be made well, though I have done no wrong.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 What man is like Job, a man who freely makes sport of God,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 And goes in the company of evil-doers, walking in the way of sinners?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he has said, It is no profit to a man to take delight in God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Now then, you wise, take note; you men of knowledge, give ear to me. Let it be far from God to do evil, and from the Ruler of all to do wrong.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For he gives to every man the reward of his work, and sees that he gets the fruit of his ways.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Truly, God does not do evil, and the Ruler of all is not a false judge.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Who put the earth into his care, or made him responsible for the world?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 If he made his spirit come back to him, taking his breath into himself again,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 All flesh would come to an end together, and man would go back to the dust.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 If you are wise, take note of this; give ear to the voice of my words.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 How may a hater of right be a ruler? and will you say that the upright Ruler of all is evil?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 He who says to a king, You are an evil-doer; and to rulers, You are sinners;
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Who has no respect for rulers, and who gives no more attention to those who have wealth than to the poor, for they are all the work of his hands.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Suddenly they come to an end, even in the middle of the night: the blow comes on the men of wealth, and they are gone, and the strong are taken away without the hand of man.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For his eyes are on the ways of a man, and he sees all his steps.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 There is no dark place, and no thick cloud, in which the workers of evil may take cover.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 For he does not give man a fixed time to come before him to be judged.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 He sends the strong to destruction without searching out their cause, and puts others in their place.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 For he has knowledge of their works, overturning them in the night, so that they are crushed.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 The evil-doers are broken by his wrath, he puts his hand on them with force before the eyes of all onlookers.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Because they did not go after him, and took no note of his ways,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 So that the cry of the poor might come up to him, and the prayer of those in need come to his ears.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Men of knowledge, and all wise men, hearing me, will say,
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job's words do not come from knowledge; they are not the fruit of wisdom.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 May Job be tested to the end, because his answers have been like those of evil men.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For in addition to his sin, he is uncontrolled in heart; before our eyes he makes sport of God, increasing his words against him.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >