< Job 14 >

1 As for man, the son of woman, his days are short and full of trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 He comes out like a flower, and is cut down: he goes in flight like a shade, and is never seen again.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Is it on such a one as this that your eyes are fixed, with the purpose of judging him?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 If only a clean thing might come out of an unclean! But it is not possible.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 If his days are ordered, and you have knowledge of the number of his months, having given him a fixed limit past which he may not go;
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Let your eyes be turned away from him, and take your hand from him, so that he may have pleasure at the end of his day, like a servant working for payment.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 For there is hope of a tree; if it is cut down, it will come to life again, and its branches will not come to an end.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Though its root may be old in the earth, and its cut-off end may be dead in the dust;
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 Still, at the smell of water, it will make buds, and put out branches like a young plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But man comes to his death and is gone: he gives up his spirit, and where is he?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 The waters go from a pool, and a river becomes waste and dry;
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 So man goes down to his last resting-place and comes not again: till the heavens come to an end, they will not be awake or come out of their sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 If only you would keep me safe in the underworld, putting me in a secret place till your wrath is past, giving me a fixed time when I might come to your memory again! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 If death takes a man, will he come to life again? All the days of my trouble I would be waiting, till the time came for me to be free.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 At the sound of your voice I would give an answer, and you would have a desire for the work of your hands.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 For now my steps are numbered by you, and my sin is not overlooked.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 My wrongdoing is corded up in a bag, and my sin is shut up safe.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 But truly a mountain falling comes to dust, and a rock is moved from its place;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 The stones are crushed small by the force of the waters; the dust of the earth is washed away by their overflowing: and so you put an end to the hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 You overcome him for ever, and he is gone; his face is changed in death, and you send him away.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 His sons come to honour, and he has no knowledge of it; they are made low, but he is not conscious of it.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 Only his flesh still has pain, and his soul is sad.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >