< Jeremiah 39 >
1 And it came about, that when Jerusalem was taken, (in the ninth year of Zedekiah, king of Judah, in the tenth month, Nebuchadrezzar, king of Babylon, with all his army, came against Jerusalem, shutting it in on every side;
A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
2 In the eleventh year of Zedekiah, in the fourth month, on the ninth day of the month, the town was broken into: )
A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
3 All the captains of the king of Babylon came in and took their places in the middle doorway of the town, Nergal-shar-ezer, ruler of Sin-magir, the Rabmag, and Nebushazban, the Rab-saris, and all the captains of the king of Babylon.
Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
4 And when Zedekiah, king of Judah, and all the men of war saw it, they went in flight from the town by night, by the way of the king's garden, through the doorway between the two walls: and they went out by the Arabah.
Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
5 But the Chaldaean army went after them and overtook Zedekiah in the lowlands of Jericho: and they made him a prisoner and took him up to Nebuchadrezzar, king of Babylon, to Riblah in the land of Hamath, to be judged by him.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
6 Then the king of Babylon put the sons of Zedekiah to death before his eyes in Riblah: and the king of Babylon put to death all the great men of Judah.
A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
7 And more than this, he put out Zedekiah's eyes, and had him put in chains to take him away to Babylon.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
8 And the Chaldaeans put the king's house on fire, as well as the houses of the people, and had the walls of Jerusalem broken down.
Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
9 Then Nebuzaradan, the captain of the armed men, took away to Babylon as prisoners, all the rest of the workmen who were still in the town, as well as those who had given themselves up to him, and all the rest of the people.
Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
10 But Nebuzaradan, the captain of the armed men, let the poorest of the people, who had nothing whatever, go on living in the land of Judah, and gave them vine-gardens and fields at the same time.
Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
11 Now Nebuchadrezzar, king of Babylon, gave orders about Jeremiah to Nebuzaradan, the captain of the armed men, saying,
To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
12 Take him and keep an eye on him and see that no evil comes to him; but do with him whatever he says to you.
“Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
13 So Nebuzaradan, the captain of the armed men, sent Nebushazban, the Rab-saris, and Nergal-shar-ezer, the Rabmag, and all the chief captains of the king of Babylon,
Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
14 And they sent and took Jeremiah out of the place of the watchmen, and gave him into the care of Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, to take him to his house: so he was living among the people.
suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
15 Now the word of the Lord came to Jeremiah while he was shut up in the place of the armed watchmen, saying,
Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
16 Go and say to Ebed-melech the Ethiopian, This is what the Lord of armies, the God of Israel, has said: See, my words will come true for this town, for evil and not for good: they will come about before your eyes on that day.
“Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
17 But I will keep you safe on that day, says the Lord: you will not be given into the hands of the men you are fearing.
Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
18 For I will certainly let you go free, and you will not be put to the sword, but your life will be given to you out of the hands of your attackers: because you have put your faith in me, says the Lord.
Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”