< Genesis 6 >

1 And after a time, when men were increasing on the earth, and had daughters,
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
2 The sons of God saw that the daughters of men were fair; and they took wives for themselves from those who were pleasing to them.
sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
3 And the Lord said, My spirit will not be in man for ever, for he is only flesh; so the days of his life will be a hundred and twenty years.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
4 There were men of great strength and size on the earth in those days; and after that, when the sons of God had connection with the daughters of men, they gave birth to children: these were the great men of old days, the men of great name.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
5 And the Lord saw that the sin of man was great on the earth, and that all the thoughts of his heart were evil.
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
6 And the Lord had sorrow because he had made man on the earth, and grief was in his heart.
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
7 And the Lord said, I will take away man, whom I have made, from the face of the earth, even man and beast and that which goes on the earth and every bird of the air; for I have sorrow for having made them.
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
8 But Noah had grace in the eyes of God.
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
9 These are the generations of Noah. Noah was an upright man and without sin in his generation: he went in the ways of God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10 And Noah had three sons, Shem, Ham, and Japheth.
Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11 And the earth was evil in God's eyes and full of violent ways.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12 And God, looking on the earth, saw that it was evil: for the way of all flesh had become evil on the earth.
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13 And God said to Noah, The end of all flesh has come; the earth is full of their violent doings, and now I will put an end to them with the earth.
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
14 Make for yourself an ark of gopher wood with rooms in it, and make it safe from the water inside and out.
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
15 And this is the way you are to make it: it is to be three hundred cubits long, fifty cubits wide, and thirty cubits high.
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
16 You are to put a window in the ark, a cubit from the roof, and a door in the side of it, and you are to make it with a lower and second and third floors.
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
17 For truly, I will send a great flow of waters over the earth, for the destruction from under the heaven of all flesh in which is the breath of life; everything on the earth will come to an end.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
18 But with you I will make an agreement; and you will come into the ark, you and your sons and your wife and your sons' wives with you.
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
19 And you will take with you into the ark two of every sort of living thing, and keep them safe with you; they will be male and female.
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
20 Two of every sort of bird and cattle and of every sort of living thing which goes on the earth will you take with you to keep them from destruction.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
21 And make a store of every sort of food for yourself and them.
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
22 And all these things Noah did; as God said, so he did.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.

< Genesis 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water