< Genesis 23 >

1 Now the years of Sarah's life were a hundred and twenty-seven.
Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
2 And Sarah's death took place in Kiriath-arba, that is, Hebron, in the land of Canaan: and Abraham went into his house, weeping and sorrowing for Sarah.
Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
3 And Abraham came from his dead and said to the children of Heth,
Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
4 I am living among you as one from a strange country: give me some land here as my property, so that I may put my dead to rest.
“Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
5 And in answer the children of Heth said to Abraham,
Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
6 My lord, truly you are a great chief among us; take the best of our resting-places for your dead; not one of us will keep back from you a place where you may put your dead to rest.
“Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
7 And Abraham got up and gave honour to the children of Heth, the people of that land.
Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
8 And he said to them, If you will let me put my dead to rest here, make a request for me to Ephron, the son of Zohar,
Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
9 That he will give me the hollow in the rock named Machpelah, which is his property at the end of his field; let him give it to me for its full price as a resting-place for my dead among you.
domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
10 Now Ephron was seated among the children of Heth: and Ephron the Hittite gave Abraham his answer in the hearing of the children of Heth, and of all those who came into his town, saying,
Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
11 No, my lord, I will give you the field with the hollow in the rock; before all the children of my people will I give it to you for a resting-place for your dead.
Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
12 And Abraham went down on his face before the people of the land.
Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
13 And Abraham said to Ephron, in the hearing of the people of the land, If only you will give ear to me, I will give you the price of the field; take it, and let me put my dead to rest there.
ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
14 So Ephron said to Abraham,
Efron ya ce wa Ibrahim,
15 My lord, give ear to me: the value of the land is four hundred shekels; what is that between me and you? so put your dead to rest there.
“Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
16 And Abraham took note of the price fixed by Ephron in the hearing of the children of Heth, and gave him four hundred shekels in current money.
Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
17 So Ephron's field at Machpelah near Mamre, with the hollow in the rock and all the trees in the field and round it,
Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
18 Became the property of Abraham before the eyes of the children of Heth and of all who came into the town.
ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
19 Then Abraham put Sarah his wife to rest in the hollow rock in the field of Machpelah near Mamre, that is, Hebron in the land of Canaan.
Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
20 And the field and the hollow rock were handed over to Abraham as his property by the children of Heth.
Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.

< Genesis 23 >