< Genesis 11 >

1 And all the earth had one language and one tongue.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 And it came about that in their wandering from the east, they came to a stretch of flat country in the land of Shinar, and there they made their living-place.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 And they said one to another, Come, let us make bricks, burning them well. And they had bricks for stone, putting them together with sticky earth.
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 And they said, Come, let us make a town, and a tower whose top will go up as high as heaven; and let us make a great name for ourselves, so that we may not be wanderers over the face of the earth.
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 And the Lord came down to see the town and the tower which the children of men were building.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 And the Lord said, See, they are all one people and have all one language; and this is only the start of what they may do: and now it will not be possible to keep them from any purpose of theirs.
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 Come, let us go down and take away the sense of their language, so that they will not be able to make themselves clear to one another.
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 So the Lord God sent them away into every part of the earth: and they gave up building their town.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 So it was named Babel, because there the Lord took away the sense of all languages and from there the Lord sent them away over all the face of the earth.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 These are the generations of Shem. Shem was a hundred years old when he became the father of Arpachshad, two years after the great flow of waters;
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 And after the birth of Arpachshad, Shem went on living for five hundred years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 And Arpachshad was thirty-five years old when he became the father of Shelah:
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 And after the birth of Shelah, Arpachshad went on living for four hundred and three years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 And Shelah was thirty years old when he became the father of Eber:
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 And after the birth of Eber, Shelah went on living for four hundred and three years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 And Eber was thirty-four years old when he became the father of Peleg:
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 And after the birth of Peleg, Eber went on living for four hundred and thirty years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 And Peleg was thirty years old when he became the father of Reu:
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 And after the birth of Reu, Peleg went on living for two hundred and nine years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 And Reu was thirty-two years old when he became the father of Serug:
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 And after the birth of Serug, Reu went on living for two hundred and seven years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 And Serug was thirty years old when he became the father of Nahor:
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 And after the birth of Nahor, Serug went on living for two hundred years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 And Nahor was twenty-nine years old when he became the father of Terah:
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 And after the birth of Terah, Nahor went on living for a hundred and nineteen years, and had sons and daughters:
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 And Terah was seventy years old when he became the father of Abram, Nahor, and Haran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 These are the generations of Terah: Terah was the father of Abram, Nahor, and Haran; and Haran was the father of Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 And death came to Haran when he was with his father Terah in the land of his birth, Ur of the Chaldees.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 And Abram and Nahor took wives for themselves: the name of Abram's wife was Sarai, and the name of Nahor's wife was Milcah, the daughter of Haran, the father of Milcah and Iscah.
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 And Sarai had no child.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 And Terah took Abram, his son, and Lot, the son of Haran, and Sarai, his daughter-in-law, the wife of his son Abram and they went out from Ur of the Chaldees, to go to the land of Canaan; and they came to Haran, and were there for some time.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 And all the years of Terah's life were two hundred and five: and Terah came to his end in Haran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.

< Genesis 11 >