< Ezra 7 >
1 Now after these things, when Artaxerxes was king of Persia, Ezra, the son of Seraiah, the son of Azariah, the son of Hilkiah,
Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
2 The son of Shallum, the son of Zadok, the son of Ahitub,
ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
3 The son of Amariah, the son of Azariah, the son of Meraioth,
ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
4 The son of Zerahiah, the son of Uzzi, the son of Bukki,
ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
5 The son of Abishua, the son of Phinehas, the son of Eleazar, the son of Aaron the chief priest:
ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
6 This Ezra went up from Babylon; and he was a scribe, expert in the law of Moses which the Lord, the God of Israel, had given: and the king, moved by the Lord his God, gave him whatever he made request for.
Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
7 And some of the children of Israel went up, with some of the priests and the Levites and the music-makers and the door-keepers and the Nethinim, to Jerusalem, in the seventh year of Artaxerxes the king.
Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
8 And he came to Jerusalem in the fifth month, in the seventh year of the king's rule.
Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
9 For, starting his journey from Babylon on the first day of the first month, he came to Jerusalem on the first day of the fifth month, by the good help of his God.
Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
10 For Ezra had given his mind to learning the law of the Lord and doing it, and to teaching his rules and decisions in Israel.
Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
11 Now this is a copy of the letter which King Artaxerxes gave to Ezra, the priest and the scribe, who put into writing the words of the orders of the Lord, and of his rules for Israel:
Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
12 Artaxerxes, king of kings, to Ezra the priest, scribe of the law of the God of heaven, all peace;
Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
13 And now it is my order that all those of the people of Israel, and their priests and Levites in my kingdom, who are ready and have a desire to go to Jerusalem, are to go with you.
Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
14 Because you are sent by the king and his seven wise men, to get knowledge about Judah and Jerusalem, as you are ordered by the law of your God which is in your hand;
Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
15 And to take with you the silver and gold freely offered by the king and his wise men to the God of Israel, whose Temple is in Jerusalem,
Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
16 As well as all the silver and gold which you get from the land of Babylon, together with the offering of the people and of the priests, freely given for the house of their God, which is in Jerusalem:
haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
17 So with this money get with care oxen, sheep, and lambs, with their meal offerings and their drink offerings, to be offered on the altar of the house of your God, which is in Jerusalem.
Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
18 And whatever seems right to you and to your brothers to do with the rest of the silver and gold, that do, as may be pleasing to your God.
Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
19 And the vessels which have been given to you for the uses of the house of your God, you are to give to the God of Jerusalem.
Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
20 And whatever more is needed for the house of your God, and which you may have to give, take it from the king's store-house.
Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
21 And I, even I, Artaxerxes the king, now give orders to all keepers of the king's money across the river, that whatever Ezra the priest, the scribe of the law of the God of heaven, may have need of from you, is to be done with all care,
Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
22 Up to a hundred talents of silver, a hundred measures of grain, a hundred measures of wine, and a hundred measures of oil, and salt without measure.
har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
23 Whatever is ordered by the God of heaven, let it be done completely for the house of the God of heaven; so that there may not be wrath against the kingdom of the king and his sons.
A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
24 In addition, we make it clear to you, that it will be against the law to put any tax or payment in goods or forced payment on any of the priests or Levites, the music-makers, door-keepers, Nethinim, or any servants of this house of God.
Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
25 And you, Ezra, by the wisdom of your God which is in you, are to put rulers and judges to have authority over all the people across the river who have knowledge of the laws of your God; and you are to give teaching to him who has no knowledge of them.
Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
26 And if anyone does not keep the law of your God and the law of the king, take care that punishment is given to him, by death or by driving him from his country or by taking away his goods or by putting him in prison.
Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
27 Praise be to the Lord, the God of our fathers, who has put such a thing into the heart of the king, to make fair the house of the Lord which is in Jerusalem;
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
28 And has given mercy to me before the king and his government and before all the king's great captains. And I was made strong by the hand of the Lord my God which was on me, and I got together out of Israel chief men to go up with me.
Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.