< Ezekiel 46 >
1 This is what the Lord has said: The doorway of the inner square looking to the east is to be shut on the six working days; but on the Sabbath it is to be open, and at the time of the new moon it is to be open.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
2 And the ruler is to go in through the covered way of the outer doorway outside, and take his place by the pillar of the doorway, and the priests will make his burned offering and his peace-offerings and he will give worship at the doorstep of the doorway; then he will go out, and the door will not be shut till the evening.
Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
3 And the people of the land are to give worship at the door of that doorway before the Lord on the Sabbaths and at the new moons.
A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
4 And the burned offering offered to the Lord by the ruler on the Sabbath day is to be six lambs without a mark on them and a male sheep without a mark;
Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
5 And the meal offering is to be an ephah for the sheep, and for the lambs whatever he is able to give, and a hin of oil to an ephah.
Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
6 And at the time of the new moon it is to be a young ox of the herd without a mark on him, and six lambs and a male sheep, all without a mark:
A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
7 And he is to give a meal offering, an ephah for the ox and an ephah for the sheep, and for the lambs whatever he is able to give, and a hin of oil to an ephah.
Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
8 And when the ruler comes in, he is to go in through the covered way of the doorway, and he is to go out by the same way.
Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
9 But when the people of the land come before the Lord at the fixed feasts, he who comes in by the north doorway to give worship is to go out by the south doorway; and he who comes in by the south doorway is to go out by the north doorway: he is not to come back by the doorway through which he went in, but is to go straight before him.
“‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
10 And the ruler, when they come in, is to come among them, and is to go out when they go out.
Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
11 At the feasts and the fixed meetings the meal offerings are to be an ephah for an ox, and an ephah for a male sheep, and for the lambs whatever he is able to give, and a hin of oil to an ephah.
“‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
12 And when the ruler makes a free offering, a burned offering or a peace-offering freely given to the Lord, the doorway looking to the east is to be made open for him, and he is to make his burned offering and his peace-offerings as he does on the Sabbath day: and he will go out; and the door will be shut after he has gone out.
Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
13 And you are to give a lamb a year old without any mark on it for a burned offering to the Lord every day: morning by morning you are to give it.
“‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
14 And you are to give, morning by morning, a meal offering with it, a sixth of an ephah and a third of a hin of oil dropped on the best meal; a meal offering offered to the Lord at all times by an eternal order.
Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
15 And they are to give the lamb and the meal offering and the oil, morning by morning, for a burned offering at all times.
Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
16 This is what the Lord has said: If the ruler gives a property to any of his sons, it is his heritage and will be the property of his sons; it is theirs for their heritage.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
17 And if he gives a part of his heritage to one of his servants, it will be his till the year of making free, and then it will go back to the ruler; for it is his sons' heritage, and is to be theirs.
In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
18 And the ruler is not to take the heritage of any of the people, driving them out of their property; he is to give a heritage to his sons out of the property which is his: so that my people may not be sent away from their property.
Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
19 And he took me through by the way in at the side of the doorway into the holy rooms which are the priests', looking to the north: and I saw a place at the side of them to the west.
Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
20 And he said to me, This is the place where the offering for error and the sin-offering are to be cooked in water by the priests, and where the meal offering is to be cooked in the oven; so that they may not be taken out into the outer square to make the people holy.
Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
21 And he took me out into the outer square and made me go by the four angles of the square; and I saw that in every angle of the open square there was a space shut in.
Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
22 In the four angles there were spaces walled in, forty cubits long and thirty wide; the four were of the same size.
A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
23 And there was a line of wall all round inside them, round all four, and boiling-places were made under it all round about.
Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
24 And he said to me, These are the boiling-rooms, where the offering of the people is cooked by the servants of the house.
Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”