< Deuteronomy 22 >
1 If you see your brother's ox or his sheep wandering, do not go by without helping, but take them back to your brother.
In kun ga saniya ko tunkiyar ɗan’uwanku wadda ta ɓace, kada ku ƙyale ta, amma ku tabbata kun komar da ita gare shi.
2 If their owner is not near, or if you are not certain who he is, then take the beast to your house and keep it till its owner comes in search of it, and then you are to give it back to him.
In ɗan’uwan ba ya zama kusa da ku, ko kuwa ba ku san shi ba, sai ku kai ta gida ku ajiye ta sai ya zo nemanta. Sa’an nan ku ba shi ita.
3 Do the same with his ass or his robe or anything which has gone from your brother's keeping and which you have come across: do not keep it to yourself.
Ku yi haka in kun sami jakin ɗan’uwanku, ko rigarsa, ko kowane abin da ya ɓace. Kada ku ƙyale shi.
4 If you see your brother's ox or his ass falling down on the road, do not go by without giving him help in lifting it up again.
In kuka ga jakin ɗan’uwanku, ko saniyarsa ya fāɗi a kan hanya, kada ku ƙyale shi. Ku taimaka, ku tā da shi.
5 It is not right for a woman to be dressed in man's clothing, or for a man to put on a woman's robe: whoever does such things is disgusting to the Lord your God.
Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata, gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yin haka.
6 If by chance you see a place which a bird has made for itself in a tree or on the earth, with young ones or eggs, and the mother bird seated on the young ones or on the eggs, do not take the mother bird with the young:
In kuka ga gidan tsuntsu kusa da hanya, ko a kan itace, ko kuma a ƙasa, mahaifiyar tsuntsun kuwa tana kwance a kan’ya’yanta, ko kuwa a kan ƙwanta, kada ku kama mahaifiyar duk da’ya’yan.
7 See that you let the mother bird go, but the young ones you may take; so it will be well for you and your life will be long.
Za ku iya kwashe’ya’yan, amma ku tabbata kun bar mahaifiyar tă tafi. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai.
8 If you are building a house, make a railing for the roof, so that the blood of any man falling from it will not come on your house.
Sa’ad da kuka gina sabon gida, ku ja masa dakali kewaye da rufinku don kada ku jawo laifin zub da jini a kan gidanku in wani ya fāɗi daga kan rufin.
9 Do not have your vine-garden planted with two sorts of seed: or all of it may become a loss, the seed you have put in as well as the increase.
Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku; in kuka yi haka, ba abin da kuka shuka ne kaɗai zai ƙazantu ba, amma har da inabinku ma.
10 Do not do your ploughing with an ox and an ass yoked together.
Kada ku haɗa bijimi da jaki su yi noma tare.
11 Do not have clothing made of two sorts of thread, wool and linen together.
Kada ku sa rigar ulu da aka gauraye da lilin aka saƙa.
12 On the four edges of your robe, with which your body is covered, put ornaments of twisted threads.
Ku yi tuntu a kusurwan huɗu na rigar da kuke sa.
13 If any man takes a wife, and having had connection with her, has no delight in her,
In mutum ya auri mace, bayan ya kwana da ita, sa’an nan ya ƙi ta
14 And says evil things about her and gives her a bad name, saying, I took this woman, and when I had connection with her it was clear to me that she was not a virgin:
ya kuma zarge ta, ya ba ta mummunan suna, yana cewa, “Na auri wannan mata, amma sa’ad da na kusace ta, ban sami tabbaci cewa ita budurwa ba ce,”
15 Then let the girl's father and mother put before the responsible men of the town, in the public place, signs that the girl was a virgin:
sai mahaifin yarinyar da mahaifiyarta su kawo shaida cewa ita budurwa ce wa dattawan gari a ƙofar garin.
16 And let the girl's father say to the responsible men, I gave my daughter to this man for his wife, but he has no love for her;
Mahaifin yarinyar zai ce wa dattawa, “Na ba da’yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.
17 And now he has put shame on her, saying that she is not a virgin; but here is the sign that she is a virgin. Then they are to put her clothing before the responsible men of the town.
Yanzu ya zage ta cewa, ‘Ban sami’yarku budurwa ba.’ Amma ga shaidar budurcin’yata.” Sa’an nan iyayenta za su shimfiɗa zanen a gaban dattawan garin,
18 Then the responsible men of the town are to give the man his punishment;
dattawan kuwa za su ɗauki mutumin su hukunta shi.
19 They will take from him a hundred shekels of silver, which are to be given to the father of the girl, because he has given an evil name to a virgin of Israel: she will go on being his wife, he may never put her away all his life.
Za su ci masa tara shekel azurfa ɗari, su ba mahaifin yarinyar, domin wannan mutum ya ba wa budurwa mutuniyar Isra’ila mummunan suna. Za tă ci gaba da zama matarsa; ba kuwa zai sake ta ba muddin ransa.
20 But if what he has said is true, and she is seen to be not a virgin,
Amma fa in zarge gaskiya ne, ba a kuwa sami shaidar budurcin yarinyar ba,
21 Then they are to make the girl come to the door of her father's house and she will be stoned to death by the men of the town, because she has done evil and put shame on Israel, by acting as a loose woman in her father's house: so you are to put away evil from among you.
sai a kawo ta a ƙofar gidan mahaifinta, a can mazan gari za su jajjefe ta da dutse har tă mutu. Ta yi abin kunya a Isra’ila ta wurin lalaci a yayinda take a gidan mahaifinta. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
22 If a man is taken in the act of going in to a married woman, the two of them, the man as well as the woman, are to be put to death: so you are to put away the evil from Israel.
In aka kama wani yana kwance da matar wani, dole a kashe dukansu biyu, wato, mutumin da ya kwana da matar da kuma matar. Dole a fid da mugu daga Isra’ila.
23 If a young virgin has given her word to be married to a man, and another man meeting her in the town, has connection with her;
In mutum ya sadu da budurwa a gari wadda aka yi alkawarin aure, ya kuma kwana da ita
24 Then you are to take the two of them to the doorway of the town, and have them stoned to death; the young virgin, because she gave no cry for help, though it was in the town, and the man, because he has put shame on his neighbour's wife: so you are to put away evil from among you.
sai ku ɗauki su biyu zuwa ƙofar wannan gari, ku jajjefe su da dutse har su mutum, za a kashe yarinyar domin tana a cikin gari ba ta kuwa yi ihu neman taimako ba, za a kashe mutumin domin ya yi lalata da matar wani. Dole ku fi da mugu daga cikinku.
25 But if the man, meeting such a virgin in the open country, takes her by force, then only the man is to be put to death;
Amma in a bayan gari ne mutumin ya sadu da yarinyar da aka yi alkawari aure, ya kuma yi mata fyaɗe, mutumin da ya yi wannan ne kaɗai zai mutu.
26 Nothing is to be done to the virgin, because there is no cause of death in her: it is the same as if a man made an attack on his neighbour and put him to death:
Kada ku yi wa yarinyar kome, ba tă yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Wannan batu ya yi kamar da na mutumin da ya fāɗa wa maƙwabcinsa ya kuma kashe shi.
27 For he came across her in the open country, and there was no one to come to the help of the virgin in answer to her cry.
Tun da ya same ta a jeji ne, wataƙila yarinyar ta yi kukan neman taimako, amma babu wani da zai cece ta.
28 If a man sees a young virgin, who has not given her word to be married to anyone, and he takes her by force and has connection with her, and discovery is made of it;
In mutum ya sadu da yarinyar da ba a yi alkawarin aurenta ba, ya kuma yi mata fyaɗe, aka kuma kama su,
29 Then the man will have to give the virgin's father fifty shekels of silver and make her his wife, because he has put shame on her; he may never put her away all his life.
sai yă biya mahaifin yarinyar shekel hamsin na azurfa. Dole yă auri yarinyar, gama ya yi lalata da ita. Ba zai taɓa sake ta ba muddin ransa.
30 A man may not take his father's wife or have sex relations with a woman who is his father's.
Kada mutum yă auri matar mahaifinsa, kada yă ƙasƙantar gādon mahaifinsa.