< 2 Kings 8 >

1 Now Elisha had said to the woman whose son he had given back to life, Go now, with all the people of your house, and get a living-place for yourselves wherever you are able; for by the word of the Lord, there will be great need of food in the land; and this will go on for seven years.
To, Elisha ya riga ya ce wa matan da ya tā da ɗanta daga matattu, “Ki kwashe iyalinki ku tafi duk inda za ku tafi na ɗan lokaci, domin Ubangiji ya sa a yi yunwa na shekara bakwai a ƙasar.”
2 So the woman got up and did as the man of God said; and she and the people of her house were living in the land of the Philistines for seven years.
Sai macen ta yi kamar yadda mutumin Allah ya faɗa. Ita da iyalinta suka tafi ƙasar Filistiyawa suka zauna shekara bakwai.
3 And when the seven years were ended, the woman came back from the land of the Philistines and went to the king with a request for her house and her land.
A ƙarshen shekara bakwai ɗin sai ta dawo daga ƙasar Filistiyawa, ta kuma tafi wajen sarki ta roƙa a mayar mata da gidanta da filinta.
4 Now the king was talking with Gehazi, the servant of the man of God, saying, Now, give me an account of all the great things Elisha has done.
Sarki kuwa yana magana da Gehazi bawan mutumin Allah, ya ce masa, “Ba ni labarin dukan abubuwan banmamakin da Elisha ya yi.”
5 And while he was giving the king the story of how Elisha had given life to the dead, the woman whose son had come back to life came to the king with a request for her house and her land. And Gehazi said, My lord king, this is the woman and this is her son, whose life Elisha gave back to him.
A sa’ad da Gehazi yana cikin ba shi labarin yadda Elisha ya tā da matacce ke nan, sai ga macen da aka tā da ɗanta daga matattu ta shigo don tă roƙi sarki yă mayar mata da gidanta da filinta. Gehazi ya ce, “Ranka yă daɗe, ai, ga macen, ga kuma ɗan da Elisha ya tā da daga matattu.”
6 And in answer to the king's questions, the woman gave him all the story. So the king gave orders to one of his unsexed servants, saying, Give her back all her property, and all the produce of her fields from the day when she went away from the land up till now.
Sarki ya tambayi macen game da al’amarin, ita kuwa ta faɗa masa. Sa’an nan ya sa wani hafsa yă dubi damuwarta ya kuma ce masa, “Ka mayar mata kome da yake nata, haɗe da dukan kuɗin da aka samo daga filin, daga ranar da ta bar ƙasar har yă zuwa yanzu.”
7 And Elisha came to Damascus; and Ben-hadad, king of Aram, was ill; and they said to him, The man of God has come.
Sai Elisha ya tafi Damaskus, Ben-Hadad mutumin Aram kuwa yana ciwo. Sa’ad da aka faɗa wa sarki, “Mutumin Allah ya hauro tun daga can zuwa nan,”
8 Then the king said to Hazael, Take an offering with you, and go to see the man of God and get directions from the Lord by him, saying, Am I going to get better from my disease?
sai ya ce wa Hazayel, “Ɗauki wannan tare da kai ka tafi ka taryi mutumin Allah. Ka nemi nufin Ubangiji ta wurinsa; ka tambaye shi, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
9 So Hazael went to see him, taking with him forty camels with offerings on their backs of every sort of good thing from Damascus; and when he came before him, he said, Your son Ben-hadad, king of Aram, has sent me to you, saying, Will I get better from this disease?
Sai Hazayel ya tafi taryen Elisha, ya ɗauka kyauta na kowane irin kaya masu kyau na Damaskus tare da shi a raƙuma arba’in. Ya shiga ya tsaya a gaban Elisha ya ce, “Ɗanka Ben-Hadad na Aram ya aike ni in tambaye ka, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
10 And Elisha said to him, Go, say to him, You will certainly get better; but the Lord has made it clear to me that only death is before him.
Elisha ya amsa ya ce, “Je ka ce masa, ‘Ba shakka za ka warke’; ammaUbangiji ya nuna mini cewa ba shakka zai mutu.”
11 And he kept his eyes fixed on him till he was shamed, and the man of God was overcome with weeping.
Sai ya zuba wa Hazayel ido har sai da Hazayel ya ji kunya. Sa’an nan mutumin Allah ya fara kuka.
12 And Hazael said, Why is my lord weeping? Then he said in answer, Because I see the evil which you will do to the children of Israel: burning down their strong towns, putting their young men to death with the sword, smashing their little ones against the stones, and cutting open the women who are with child.
Hazayel ya ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake kuka?” Elisha ya amsa, “Domin na san illar da za ka yi wa Isra’ilawa. Za ka ƙona biranensu masu katanga, ka karkashe majiya ƙarfinsu da takobi, ka fyaffyaɗe ƙananan yaransu da ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”
13 And Hazael said, How is it possible that your servant, who is only a dog, will do this great thing? And Elisha said, The Lord has made it clear to me that you will be king over Aram.
Hazayel ya ce, “Yaya bawanka, wanda yake kare kawai, zai iya aikata wannan irin abu?” Elisha ya ce, “Ubangiji ya nuna mini cewa za ka zama sarkin Aram.”
14 Then he went away from Elisha and came in to his master, who said to him, What did Elisha say to you? And his answer was, He said that you would certainly get well.
Sai Hazayel ya rabu da Elisha ya koma wurin maigidansa. Da Ben-Hadad ya yi tambaya, “Me Elisha ya ce maka?” Sai Hazayel ya amsa, “Ya faɗa mini cewa tabbatacce za ka warke.”
15 Now on the day after, Hazael took the bed-cover, and making it wet with water, put it over Ben-hadad's face, causing his death: and Hazael became king in his place.
Amma kashegari sai ya ɗauki tsumma mai kauri, ya jiƙa shi, ya rufe fuskar sarki da shi, har sai da sarki ya mutu. Sai Hazayel ya gāje shi a matsayin sarki.
16 In the fifth year of Joram, the son of Ahab, king of Israel, Jehoram, the son of Jehoshaphat, king of Judah, became king.
A shekara ta biyar ta mulkin Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, sa’ad da Yehoshafat yake sarautar Yahuda, Yoram ɗan Yehoshafat, ya fara mulkinsa a matsayin sarkin Yahuda.
17 He was thirty-two years old when he became king; and he was ruling in Jerusalem for eight years.
Yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki na tsawon shekara takwas a Urushalima.
18 He went in the ways of the kings of Israel, as the family of Ahab did: for the daughter of Ahab was his wife; and he did evil in the eyes of the Lord.
Ya bi gurbin sarakunan Isra’ila, yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya yi mugunta a gaban Ubangiji.
19 But it was not the Lord's purpose to send destruction on Judah, because of David his servant, to whom he had given his word that he would have a light for ever.
Duk da haka, saboda bawansa Dawuda, Ubangiji bai ragargaza Yahuda ba. Ya riga ya yi alkawari zai bar wa Dawuda magāji har abada.
20 In his time, Edom made themselves free from the rule of Judah, and took a king for themselves.
A kwanakin Yoram, Edom ta yi wa Yahuda tawaye, ta naɗa wa kanta sarki.
21 Then Joram went over to Zair, with all his war-carriages; ... made an attack by night on the Edomites, whose forces were all round him, ... the captains of the war-carriages; and the people went in flight to their tents.
Saboda haka Yehoram ya tafi Zayir da dukan kekunan yaƙinsa. Sojojin Edom suka kewaye shi a can, amma da dare sai Yoram ya ɓarke ya gudu, sojojinsa kuma suka watse zuwa gidajensu.
22 So Edom made themselves free from the rule of Judah to this day. And at the same time, Libnah made itself free.
Har yă zuwa yau, Edom tana yi wa Yahuda tawaye. A lokaci ɗaya ne Libna ma ta yi tawaye.
23 Now the rest of the acts of Joram, and all he did, are they not recorded in the book of the history of the kings of Judah?
Game da waɗansu abubuwan da suka faru a zamanin Yoram, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?
24 And Joram went to rest with his fathers and was put into the earth with his fathers in the town of David: and Ahaziah his son became king in his place.
Yoram ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda. Sai Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 In the twelfth year that Joram, the son of Ahab, was king of Israel, Ahaziah, the son of Jehoram, king of Judah, became king;
A shekara ta goma sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya fara mulki.
26 Ahaziah was twenty-two years old when he became king, and he was ruling in Jerusalem for one year. His mother's name was Athaliah, the daughter of Omri, king of Israel.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya, jikanyar Omri, sarkin Isra’ila.
27 He went in the ways of the family of Ahab, and did evil in the eyes of the Lord as the family of Ahab did, for he was a son-in-law of the family of Ahab.
Ya bi gurbin gidan Ahab, ya yi mugunta a gaban Ubangiji yadda gida Ahab ta yi, gama yana da dangantaka ta aure da gidan Ahab.
28 He went with Joram, the son of Ahab, to make war on Hazael, king of Aram, at Ramoth-gilead: and Joram was wounded by the Aramaeans.
Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab don su yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
29 So King Joram went back to Jezreel to get well from the wounds which the bowmen had given him at Ramah, when he was fighting against Hazael, king of Aram. And Ahaziah, the son of Jehoram, king of Judah, went down to see Joram, the son of Ahab, in Jezreel, because he was ill.
saboda haka Sarki Yoram ya koma zuwa Yezireyel don yă yi jinyar raunin da Arameyawa suka ji masa a Rama a yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel yă dubi Yoram ɗan Ahab domin an yi masa rauni.

< 2 Kings 8 >