< 2 Chronicles 26 >
1 Then all the people of Judah took Uzziah, who was sixteen years old, and made him king in place of his father Amaziah.
Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
2 He was the builder of Eloth, which he got back for Judah after the death of the king.
Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
3 Uzziah was sixteen years old when he became king, and he was ruling in Jerusalem for fifty-two years; his mother's name was Jechiliah of Jerusalem.
Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
4 He did what was right in the eyes of the Lord, as his father Amaziah had done.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
5 He gave himself to searching after God in the days of Zechariah, who made men wise in the fear of God; and as long as he was true to the Lord, God made things go well for him.
Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
6 He went out and made war against the Philistines, pulling down the walls of Gath and Jabneh and Ashdod, and building towns in the country round Ashdod and among the Philistines.
Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
7 And God gave him help against the Philistines, and against the Arabians living in Gur-baal, and against the Meunim.
Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
8 The Ammonites gave offerings to Uzziah: and news of him went out as far as the limit of Egypt; for he became very great in power.
Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
9 Uzziah made towers in Jerusalem, at the doorway in the angle and at the doorway in the valley and at the turn of the wall, arming them.
Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
10 And he put up towers in the waste land and made places for storing water, for he had much cattle, in the low hills and in the table land; and he had farmers and vine-keepers in the mountains and in the fertile land, for he was a lover of farming.
Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
11 In addition, Uzziah had an army of fighting-men who went out to war in bands, as they had been listed by Jeiel the scribe and Maaseiah the ruler, under the authority of Hananiah, one of the king's captains.
Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
12 The heads of families, the strong men of war, were two thousand, six hundred.
Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
13 And under their orders was a trained army of three hundred and seven thousand, five hundred, of great strength in war, helping the king against any who came against him.
A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
14 And Uzziah had all these forces armed with body-covers and spears and head-covers and coats of metal and bows and stones for sending from leather bands.
Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
15 And in Jerusalem he made machines, the invention of expert men, to be placed on the towers and angles of the walls for sending arrows and great stones. And his name was honoured far and wide; for he was greatly helped till he was strong.
A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
16 But when he had become strong, his heart was lifted up in pride, causing his destruction; and he did evil against the Lord his God; for he went into the Temple of the Lord for the purpose of burning perfumes on the altar of perfumes.
Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
17 And Azariah the priest went in after him, with eighty of the Lord's priests, who were strong men;
Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
18 And they made protests to Uzziah the king, and said to him, The burning of perfumes, Uzziah, is not your business but that of the priests, the sons of Aaron, who have been made holy for this work: go out of the holy place, for you have done wrong, and it will not be to your honour before God.
Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
19 Then Uzziah was angry; and he had in his hand a vessel for burning perfume; and while his wrath was bitter against the priests, the mark of the leper's disease came out on his brow, before the eyes of the priests in the house of the Lord by the altar of perfumes.
Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
20 And Azariah, the chief priest, and all the priests, looking at him, saw the mark of the leper on his brow, and they sent him out quickly and he himself went out straight away, for the Lord's punishment had come on him.
Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
21 So King Uzziah was a leper till the day of his death, living separately in his private house; for he was cut off from the house of God; and Jotham his son was ruling over his house, judging the people of the land.
Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
22 Now the rest of the acts of Uzziah, first and last, were recorded by Isaiah the prophet, the son of Amoz.
Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
23 So Uzziah went to rest with his fathers; and they put his body into the earth in the field used for the resting-place of the kings, for they said, He is a leper: and Jotham his son became king in his place.
Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.