< 1 Samuel 26 >

1 And the Ziphites came to Saul at Gibeah, and said, Is not David waiting secretly near us in the hill of Hachilah, before the waste land?
Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
2 Then Saul went down to the waste land of Ziph, taking with him three thousand of the best men of Israel, to make search for David in the waste land of Ziph.
Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
3 And Saul put up his tents on the hill of Hachilah, which is in front of the waste land on the road. But David was in the waste land, and he saw that Saul was coming after him.
Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
4 And so David sent out watchers, and got word from them that Saul was certainly coming.
sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
5 And David got up and came to the place where Saul's tents were: and David had a view of the place where Saul was sleeping with Abner, the son of Ner, the captain of his army: and Saul was sleeping inside the ring of carts, and the tents of the people were all round him.
Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
6 Then David said to Ahimelech the Hittite, and to Abishai, the son of Zeruiah, brother of Joab, Who will go down with me to the tents of Saul? And Abishai said, I will go down with you.
Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
7 So David and Abishai came down to the army by night: and Saul was sleeping inside the ring of carts with his spear planted in the earth by his head: and Abner and the people were sleeping round him.
Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
8 Then Abishai said to David, God has given up your hater into your hands today; now let me give him one blow through to the earth with his spear, and there will be no need to give him a second.
Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
9 And David said to Abishai Do not put him to death; for who, without sin, may put out his hand against the man on whom the Lord has put the holy oil?
Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
10 And David said, By the living Lord, the Lord will send destruction on him; the natural day of his death will come, or he will go into the fight and come to his end.
Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
11 Never will my hand be stretched out against the man marked with the holy oil; but take the spear which is by his head and the vessel of water, and let us go.
Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
12 So David took the spear and the vessel of water from Saul's head; and they got away without any man seeing them, or being conscious of their coming, or awaking; for they were all sleeping because a deep sleep from the Lord had come on them.
Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
13 Then David went over to the other side, and took his place on the top of a mountain some distance away, with a great space between them;
Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
14 And crying out to the people and to Abner, the son of Ner, David said, Have you no answer to give, Abner? Then Abner said, Who is that crying out to the king?
Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
15 And David said to Abner, Are you not a man of war? is there any other like you in Israel? why then have you not kept watch over your lord the king? for one of the people came in to put the king your lord to death.
Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
16 What you have done is not good. By the living Lord, death is the right fate for you, because you have not kept watch over your lord, the man on whom the Lord has put the holy oil. Now see, where is the king's spear, and the vessel of water which was by his head?
Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
17 And Saul, conscious that the voice was David's, said, Is that your voice, David, my son? And David said, It is my voice, O my lord king.
Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
18 And he said, Why does my lord go armed against his servant? what have I done? or what evil is there in me?
Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
19 Let my lord the king give ear now to the words of his servant. If it is the Lord who is moving you against me, let him take an offering: but if it is the children of men, may they be cursed before the Lord, for driving me out today and keeping me from my place in the heritage of the Lord, saying, Go, be the servant of other gods.
To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
20 Then do not let my blood be drained out on the earth away from the face of the Lord: for the king of Israel has come out to take my life, like one going after birds in the mountains.
Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
21 Then Saul said, I have done wrong: come back to me, David my son: I will do you no more wrong, because my life was dear to you today truly, I have been foolish and my error is very great.
Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
22 Then David said, Here is the king's spear! let one of the young men come over and get it.
Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
23 And the Lord will give to every man the reward of his righteousness and his faith: because the Lord gave you into my hands today, and I would not put out my hand against the man who has been marked with the holy oil.
Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
24 And so, as your life was dear to me today, may my life be dear to the Lord, and may he make me free from all my troubles.
Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
25 Then Saul said to David, May a blessing be on you, David, my son; you will do great things and without doubt you will overcome. Then David went on his way, and Saul went back to his place.
Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.

< 1 Samuel 26 >