< 1 John 3 >

1 See what great love the Father has given us in naming us the children of God; and such we are. For this reason the world does not see who we are, because it did not see who he was.
Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba.
2 My loved ones, now we are children of God, and at present it is not clear what we are to be. We are certain that at his revelation we will be like him; for we will see him as he is.
Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake.
3 And everyone who has this hope in him makes himself holy, even as he is holy.
Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.
4 Everyone who is a sinner goes against the law, for sin is going against the law.
Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne.
5 And you have knowledge that he came to take away sin: and in him there is no sin.
Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi.
6 Anyone who is in him does no sin; anyone who is a sinner has not seen him and has no knowledge of him.
Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.
7 My little children, let no man take you out of the true way: he who does righteousness is upright, even as he is upright;
'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali.
8 The sinner is a child of the Evil One; for the Evil One has been a sinner from the first. And the Son of God was seen on earth so that he might put an end to the works of the Evil One.
Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.
9 Anyone who is a child of God does no sin, because he still has God's seed in him; he is not able to be a sinner, because God is his Father.
Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah.
10 In this way it is clear who are the children of God and who are the children of the Evil One; anyone who does not do righteousness or who has no love for his brother, is not a child of God.
Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.
11 Because this is the word which was given to you from the first, that we are to have love for one another;
Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu,
12 Not being of the Evil One like Cain, who put his brother to death. And why did he put him to death? Because his works were evil and his brother's works were good.
ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.
13 Do not be surprised, my brothers, if the world has no love for you.
Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku.
14 We are conscious that we have come out of death into life because of our love for the brothers. He who has no love is still in death.
Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne.
15 Anyone who has hate for his brother is a taker of life, and you may be certain that no taker of life has eternal life in him. (aiōnios g166)
Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai. (aiōnios g166)
16 In this we see what love is, because he gave his life for us; and it is right for us to give our lives for the brothers.
Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu.
17 But if a man has this world's goods, and sees that his brother is in need, and keeps his heart shut against his brother, how is it possible for the love of God to be in him?
Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa?
18 My little children, do not let our love be in word and in tongue, but let it be in act and in good faith.
'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.
19 In this way we may be certain that we are true, and may give our heart comfort before him,
Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa.
20 When our heart says that we have done wrong; because God is greater than our heart, and has knowledge of all things.
Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome.
21 My loved ones, if our heart does not say that we have done wrong, we have no fear before him;
Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah.
22 And he gives us all our requests, because we keep his laws and do the things which are pleasing in his eyes.
Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.
23 And this is his law, that we have faith in the name of his Son Jesus Christ, and love for one another, even as he said to us.
Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka.
24 He who keeps his laws is in God and God is in him. And the Spirit which he gave us is our witness that he is in us.
Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.

< 1 John 3 >