< 1 Chronicles 5 >

1 And the sons of Reuben, the oldest son of Israel, (for he was the oldest son, but, because he made his father's bride-bed unclean, his birthright was given to the sons of Joseph, the son of Israel; but he is not to be given the place of the oldest.
’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
2 Though Judah became stronger than his brothers, and from him came the ruler, the birthright was Joseph's: )
ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
3 The sons of Reuben, the oldest son of Israel: Hanoch and Pallu, Hezron and Carmi.
’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
4 The sons of Joel: Shemaiah his son, Gog his son, Shimei his son,
Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
5 Micah his son, Reaiah his son, Baal his son,
Mika, Reyahiya, Ba’al,
6 Beerah his son, whom Tiglath-pileser, king of Assyria, took away as a prisoner: he was chief of the Reubenites.
da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
7 And his brothers by their families, when the list of their generations was made up: the chief, Jeiel, and Zechariah,
Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
8 And Bela, the son of Azaz, the son of Shema, the son of Joel, who was living in Aroer, as far as Nebo and Baal-meon;
da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
9 And to the east his limits went as far as the starting point of the waste land, ending at the river Euphrates, because their cattle were increased in number in the land of Gilead.
Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
10 And in the days of Saul they made war on the Hagarites, and overcame them; and they put up their tents through all the land east of Gilead.
A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
11 And the sons of Gad were living opposite to them, in the land of Bashan as far as Salecah:
Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
12 Joel the chief, and Shapham the second, and Janai and Shaphat in Bashan;
Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
13 And their brothers, the men of their family: Michael and Meshullam and Sheba and Jorai and Jacan and Zia and Eber, seven of them.
Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
14 These were the sons of Abihail, the son of Huri, the son of Jaroah, the son of Gilead, the son of Michael, the son of Jeshishai, the son of Jahdo, the son of Buz;
Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
15 Ahi, the son of Abdiel, the son of Guni, head of their families.
Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
16 And they were living in Gilead in Bashan, in its small towns and in all the grass-land of Sirion as far as its limits.
Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
17 All these were listed under the names of their families, in the time of Jotham, king of Judah, and in the time of Jeroboam, king of Israel.
Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
18 There were forty-four thousand, seven hundred and sixty of the sons of Reuben and of the Gadites and of the half-tribe of Manasseh, all strong men, expert in the use of the body-cover, the sword, and the bow, and in the art of war, all able to take up arms.
Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
19 And they went to war against the Hagarites, with Jetur and Naphish and Nodab.
Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
20 And they were helped against them, so that the Hagarites, and those with them, were given into their power. For they sent up prayers to God in the fight, and he gave ear to them, because they put their faith in him.
Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
21 And they took away their cattle: fifty thousand camels, two hundred and fifty thousand sheep, and two thousand asses, and a hundred thousand men.
Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
22 And a very great number went to their death, because the war was God's purpose. And they went on living in their place till they were taken away as prisoners.
waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
23 And the men of the half-tribe of Manasseh were living in the land: and their numbers were increased till all the land from Bashan to Baal-hermon and Senir and the mountain Hermon was theirs.
Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
24 And these were the heads of their families: Epher and Ishi and Eliel and Azriel and Jeremiah and Hodaviah and Jahdiel, men of war, of great name, heads of families.
Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
25 And they did evil against the God of their fathers, worshipping the gods of the people of the land, whom God had put to destruction before them.
Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
26 And the God of Israel put an impulse into the heart of Pul, king of Assyria, and of Tiglath-pileser, king of Assyria, who took them away as prisoners, all the Reubenites and the Gadites and the half-tribe of Manasseh, to Halah and Habor and Hara and to the river of Gozan, to this day.
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.

< 1 Chronicles 5 >