< Romans 9 >

1 I speak the truth in Christ; I am not lying, as confirmed by my conscience in the Holy Spirit.
Gaskiya ne nake gaskiya nake fada cikin Almasihu. Ba karya nake yi ba. Lamirina, na shaida a cikin Ruhu Mai Tsarki.
2 I have deep sorrow and unceasing anguish in my heart.
cewa ina da matukar bakin-ciki da takaici marar karewa a zuciyata.
3 For I could wish that I myself were cursed and cut off from Christ for the sake of my brothers, my own flesh and blood,
Dama ace, a la'anta ni, in rabu da Almasihu saboda 'yan'uwana, wato dangina da suke zuriyata bisa ga jiki.
4 the people of Israel. Theirs is the adoption as sons; theirs the divine glory and the covenants; theirs the giving of the law, the temple worship, and the promises.
Sune Isra'ilawa, sun sami karbuwa, da daukaka, da baiwar shari'a, da yi wa Allah sujada, da alkawarai.
5 Theirs are the patriarchs, and from them proceeds the human descent of Christ, who is God over all, forever worthy of praise! Amen. (aiōn g165)
Dukkan ubanni nasu ne daga cikinsu Almasihu ya fito bisa ga jiki- wanda shi ke Allah bisa kowa. Yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin. (aiōn g165)
6 It is not as though God’s word has failed. For not all who are descended from Israel are Israel.
Amma ba wai alkawarin Allah ya kasa ba ne, ba dukkan Isra'ilawa ne suke Isra'ilawa na gaskiya ba.
7 Nor because they are Abraham’s descendants are they all his children. On the contrary, “Through Isaac your offspring will be reckoned.”
Haka nan, ba dukkan zuriyar Ibrahim ne 'ya'yansa ba. Amma ''ta wurin Ishiyaku ne za'a kira zuriyarka.''
8 So it is not the children of the flesh who are God’s children, but it is the children of the promise who are regarded as offspring.
Yana nuna mana cewa ba 'ya'yan jiki su ne 'ya'yan Allah ba. Amma 'ya'yan alkawari ne ake kirga su, kuma aka kebe su.
9 For this is what the promise stated: “At the appointed time I will return, and Sarah will have a son.”
Wanna ce kalmar alkawari, ''badi warhaka zan dawo, Saratu kuwa zata sami da.''
10 Not only that, but Rebecca’s children were conceived by one man, our father Isaac.
Amma ba wannan kadai ba, bayan Rifkatu ta dauki ciki daga gun mijinta, ubammu Ishiyaku.
11 Yet before the twins were born or had done anything good or bad, in order that God’s plan of election might stand,
Yaran nan kafin ma a haife su, balle ma a ce sun yi wani abu mai kyau ko laifi, saboda zaben da Allah yayi, bai danganta da abin da suka yi ba, ko don aiki ba, amma don shine mai kira—
12 not by works but by Him who calls, she was told, “The older will serve the younger.”
kamar yadda Ya ce, mata, “babban zaya yiwa karamin bauta,'' haka nassi yace,
13 So it is written: “Jacob I loved, but Esau I hated.”
''Kamar yadda aka rubuta: “Yakubu na ke kauna, amma Isuwa na ki shi.”
14 What then shall we say? Is God unjust? Certainly not!
To me zamu ce kenan? Allah ya yi rashin adalci kenan? Ko kadan.
15 For He says to Moses: “I will have mercy on whom I have mercy, and I will have compassion on whom I have compassion.”
Gama ya ce wa Musa, ''Ina nuna jinkai ga wanda zan yi wa jinkai, zan ji tausayi ga wanda zan tausaya masa.''
16 So then, it does not depend on man’s desire or effort, but on God’s mercy.
Saboda haka, ba don wanda ke da aniya ba ne, ko kuwa wanda yake kokari ba, amma saboda Allah mai nuna jinkai.
17 For the Scripture says to Pharaoh: “I raised you up for this very purpose, that I might display My power in you, and that My name might be proclaimed in all the earth.”
Gama nassi ya ce da Fir'auna, '' Saboda wannan dalilin ne, na tada kai, don in nuna ikona mai karfi a kanka, don sunana ya yadu ga dukkan duniya.''
18 Therefore God has mercy on whom He wants to have mercy, and He hardens whom He wants to harden.
Ta haka Allah ya nuna jinkansa ga wanda ya so, ya taurarar da zuciyar wanda ya ga dama.
19 One of you will say to me, “Then why does God still find fault? For who can resist His will?”
Za kuce mani, to don me, ''Yake kama mu da llaifi? Wa ya taba yin jayayya da nufinsa?''
20 But who are you, O man, to talk back to God? Shall what is formed say to Him who formed it, “Why did You make me like this?”
In ma mun duba, kai mutum wanene kai da zaka ja da Allah? Ko abin da aka gina zai ce wa magininsa, ''Don me yasa ka ginani haka?''
21 Does not the potter have the right to make from the same lump of clay one vessel for special occasions and another for common use?
Ko maginin ba shi da iko akan yimbu daya da zai gina tukunya mai daraja, wata kuma tukunyar don kowanne irin aiki?
22 What if God, intending to show His wrath and make His power known, bore with great patience the vessels of His wrath, prepared for destruction?
In ace Allah, dake niyyar nuna fushinsa da ikonsa, ya sanu, sai ya jure da matukar hakuri mai yawa da tukwanen fushi da ya shirya don hallakarwar fa?
23 What if He did this to make the riches of His glory known to the vessels of His mercy, whom He prepared in advance for glory—
To ko ma ya yi haka don ya nuna yalwar daukakarsa da take dauke da alheri, wanda ya shirya don daukakarsa tun farko?
24 including us, whom He has called not only from the Jews, but also from the Gentiles?
Zai yiwu ma ya yi haka ne domin mu, mu da ya kira, ba ma daga cikin Yahudawa kadai ba, amma har ma daga cikin al'ummai?
25 As He says in Hosea: “I will call them ‘My People’ who are not My people, and I will call her ‘My Beloved’ who is not My beloved,”
Kamar yadda ya ce a cikin littafin Yusha'u: ''zan kira wadanda ba mutanena ba mutanena, da kuma kaunatattunta wadanda ba kaunatattu ba.
26 and, “It will happen that in the very place where it was said to them, ‘You are not My people,’ they will be called ‘sons of the living God.’”
Zai zama kuma a inda aka ce da su, “ku ba mutanena bane, za a kisa su 'ya'yan Allah mai rai.”'
27 Isaiah cries out concerning Israel: “Though the number of the Israelites is like the sand of the sea, only the remnant will be saved.
Ishaya ya yi kira game da Isra'ila, ''in a ce yawan 'ya'yan Isra'ila zasu zama kamar yashi a bakin teku, ragowarsu ne kawai za su sami ceto.
28 For the Lord will carry out His sentence on the earth thoroughly and decisively.”
Ubangiji zai tabbatar da cikar kalmarsa a duniya, ba kuwa da dadewa ba.
29 It is just as Isaiah foretold: “Unless the Lord of Hosts had left us descendants, we would have become like Sodom, we would have resembled Gomorrah.”
Yadda Ishaya ya rubuta ada, ''In da ba Ubangiji mai runduna bai bar mana zuriya ba, da zamu zama kamar Saduma, da kuma an maida mu kamar Gomarata.
30 What then will we say? That the Gentiles, who did not pursue righteousness, have obtained it, a righteousness that is by faith;
To me za mu ce kenan? Ko al'ummai, da ba sa neman adalci, sun samu adalci ta wurin bangaskiya.
31 but Israel, who pursued a law of righteousness, has not attained it.
Amma Isra'ila, wadanda suka nemi adalcinsu ta wurin shari'a, ba su kai ga gaci ba.
32 Why not? Because their pursuit was not by faith, but as if it were by works. They stumbled over the stumbling stone,
To don me? don ba su neme shi da bangaskiya ba, amma ta ayyuka. Sun yi tuntube a kan dutse da zai sa laifi.
33 as it is written: “See, I lay in Zion a stone of stumbling and a rock of offense; and the one who believes in Him will never be put to shame.”
Kamar yadda aka rubuta, “Ga, shi na ajiye dutse a kan Sihiyona dutsen tuntube mai sa laifi. Ga wanda ya bada gaskiya gare shi ba zai ji kunya ba.”

< Romans 9 >