< Revelation 9 >
1 Then the fifth angel sounded his trumpet, and I saw a star that had fallen from heaven to earth, and it was given the key to the pit of the Abyss. (Abyssos )
Sa'annan mala'ika na biyar ya busa kahonsa. Na ga tauraro daga sama da ya fado zuwa duniya. An ba tauraron nan mabudin hanyar rami marar iyaka. (Abyssos )
2 The star opened the pit of the Abyss, and smoke rose out of it like the smoke of a great furnace, and the sun and the air were darkened by the smoke from the pit. (Abyssos )
Ya bude hanyar rami marar iyaka, sai hayaki ya fito daga kofar kamar hayaki daga babban ramin wuta. Rana da iska suka juya duhu, sabili da hayakin da ke fitowa daga kofar ramin. (Abyssos )
3 And out of the smoke, locusts descended on the earth, and they were given power like that of the scorpions of the earth.
Daga cikin hayakin kuwa sai ga fari sun fito zuwa duniya, aka ba su iko kamar na kunamai cikin duniya.
4 They were told not to harm the grass of the earth or any plant or tree, but only those who did not have the seal of God on their foreheads.
Aka gaya masu kada su yi wa ciyayi da kowanne koren ganye ko itace illa, sai dai mutanen da basu da hatimin Allah a goshinsu.
5 The locusts were not given power to kill them, but only to torment them for five months, and their torment was like the stinging of a scorpion.
Ba a basu izini su kashe wadannan mutane ba, sai dai su azabtar da su na watani biyar. Zafinsu kuwa zai zama kamar na cizon kunama idan ta harbi mutum.
6 In those days men will seek death and will not find it; they will long to die, but death will escape them.
A kwanakin nan mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba. Za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za ta guje su.
7 And the locusts looked like horses prepared for battle, with something like crowns of gold on their heads, and faces like the faces of men.
Farin kuwa suna kama da dawakai da aka shirya domin yaki. A bisa kansu akwai wani abu kamar rawanan zinariya, fuskokinsu kuma kamar na 'yan adam.
8 They had hair like that of women, and teeth like those of lions.
Gashinsu kuma kamar na mata yake, hakoransu kamar hakoran zaki.
9 They also had thoraxes like breastplates of iron, and the sound of their wings was like the roar of many horses and chariots rushing into battle.
Sulkunansu kuma kamar na karfe, karar fikafikansu kuma kamar karar kekunan dawakin yaki masu yawa da dawakai da aka shirya domin zuwa yaki.
10 They had tails with stingers like scorpions, which had the power to injure people for five months.
Suna da wutsiya da kari kamar kunamai; A wutsiyar su kuma suna da ikon da zai azabtar da mutane na tsawon wata biyar.
11 They were ruled by a king, the angel of the Abyss. His name in Hebrew is Abaddon, and in Greek it is Apollyon. (Abyssos )
Suna da wani kamar sarki a kansu, mala'ikan rami marar iyaka. Sunansa da Ibraniyanci Abadon, da Helenanci kuma Afoliyon. (Abyssos )
12 The first woe has passed. Behold, two woes are still to follow.
Bala'i na fari ya wuce. Duba! Bayan wannan akwai masifu guda biyu masu zuwa.
13 Then the sixth angel sounded his trumpet, and I heard a voice from the four horns of the golden altar before God
Mala'ika na shida ya busa kahonsa, sai na ji murya daga kahonin bagadin zinariya da ke gaban Allah.
14 saying to the sixth angel with the trumpet, “Release the four angels who are bound at the great river Euphrates.”
Muryar ta ce wa mala'ika na shida da ke rike da kahon, “Kwance mala'ikun nan hudu da ke daure a babban kogin Yufiretis,''
15 So the four angels who had been prepared for this hour and day and month and year were released to kill a third of mankind.
Mala'iku hudun da aka shirya domin wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da kuma wannan shekara, aka sake su su kashe daya bisa uku na 'yan adam.
16 And the number of mounted troops was two hundred million; I heard their number.
Yawan sojoji da ke kan dawakai shine 200, 000, 000. Na ji adadin su.
17 Now the horses and riders in my vision looked like this: The riders had breastplates the colors of fire, sapphire, and sulfur. The heads of the horses were like the heads of lions, and out of their mouths proceeded fire, smoke, and sulfur.
Haka na ga dawakan a cikin wahayina da mahayansu: Sulkunansu jawur kamar wuta, bakin shudi, da kuma ruwan doruwa. Kawunan dawakan suna kama da na zakuna, daga bakunansu kuma wuta, da hayaki da farar wuta suka fito.
18 A third of mankind was killed by the three plagues of fire, smoke, and sulfur that proceeded from their mouths.
Aka kashe daya bisa uku na mutane ta annoban nan uku: wuta, hayaki da farar wuta da suka fito daka bakunansu.
19 For the power of the horses was in their mouths and in their tails; indeed, their tails were like snakes, having heads with which to inflict harm.
Domin iko na dawakan na bakunansu da wutsiyoyinsu - domin wutsiyoyinsu suna kama da macizai, kuma suna da kawuna wadanda dasu suke ji wa mutane rauni.
20 Now the rest of mankind who were not killed by these plagues still did not repent of the works of their hands. They did not stop worshiping demons and idols of gold, silver, bronze, stone, and wood, which cannot see or hear or walk.
Sauran 'yan adam, da ba a kashe su ta wannan annoba ba, basu tuba daga ayyukan da suka yi ba. Basu kuma daina bautar aljanu da gumakan zinariya, da azurfa, da tagulla, da dutse, da itace ba - abubuwan da ba su gani, ji, ko tafiya.
21 Furthermore, they did not repent of their murder, sorcery, sexual immorality, and theft.
Basu kuma tuba ba daga kisan kai, sihiri, fasikanci, ko kuma ayyukansu na sata ba.