< Psalms 87 >

1 A Psalm of the sons of Korah. A song. He has founded His city on the holy mountains.
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 The LORD loves the gates of Zion more than all the dwellings of Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Glorious things are ascribed to you, O city of God.
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 “I will mention Rahab and Babylon among those who know Me— along with Philistia, Tyre, and Cush — when I say, ‘This one was born in Zion.’”
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 And it will be said of Zion: “This one and that one were born in her, and the Most High Himself will establish her.”
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 The LORD will record in the register of the peoples: “This one was born in Zion.”
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 Singers and pipers will proclaim, “All my springs of joy are in You.”
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”

< Psalms 87 >