< Psalms 80 >
1 For the choirmaster. To the tune of “The Lilies of the Covenant.” A Psalm of Asaph. Hear us, O Shepherd of Israel, who leads Joseph like a flock; You who sit enthroned between the cherubim, shine forth
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 before Ephraim, Benjamin, and Manasseh. Rally Your mighty power and come to save us.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Restore us, O God, and cause Your face to shine upon us, that we may be saved.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 O LORD God of Hosts, how long will Your anger smolder against the prayers of Your people?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 You fed them with the bread of tears and made them drink the full measure of their tears.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 You make us contend with our neighbors; our enemies mock us.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 Restore us, O God of Hosts, and cause Your face to shine upon us, that we may be saved.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 You uprooted a vine from Egypt; You drove out the nations and transplanted it.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 You cleared the ground for it, and it took root and filled the land.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 The mountains were covered by its shade, and the mighty cedars with its branches.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 It sent out its branches to the Sea, and its shoots toward the River.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 Why have You broken down its walls, so that all who pass by pick its fruit?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 The boar from the forest ravages it, and the creatures of the field feed upon it.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Return, O God of Hosts, we pray! Look down from heaven and see! Attend to this vine—
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 the root Your right hand has planted, the son You have raised up for Yourself.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 Your vine has been cut down and burned; they perish at the rebuke of Your countenance.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Let Your hand be upon the man at Your right hand, on the son of man You have raised up for Yourself.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 Then we will not turn away from You; revive us, and we will call on Your name.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 Restore us, O LORD God of Hosts; cause Your face to shine upon us, that we may be saved.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.