< Psalms 73 >

1 A Psalm of Asaph. Surely God is good to Israel, to those who are pure in heart.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But as for me, my feet had almost stumbled; my steps had nearly slipped.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For I envied the arrogant when I saw the prosperity of the wicked.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 They have no struggle in their death; their bodies are well-fed.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 They are free of the burdens others carry; they are not afflicted like other men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore pride is their necklace; a garment of violence covers them.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 From their prosperity proceeds iniquity; the imaginations of their hearts run wild.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They mock and speak with malice; with arrogance they threaten oppression.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They set their mouths against the heavens, and their tongues strut across the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 So their people return to this place and drink up waters in abundance.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 The wicked say, “How can God know? Does the Most High have knowledge?”
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold, these are the wicked— always carefree as they increase their wealth.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Surely in vain I have kept my heart pure; in innocence I have washed my hands.
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 For I am afflicted all day long and punished every morning.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I had said, “I will speak this way,” then I would have betrayed Your children.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 When I tried to understand all this, it was troublesome in my sight
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 until I entered God’s sanctuary; then I discerned their end.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Surely You set them on slick ground; You cast them down into ruin.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How suddenly they are laid waste, completely swept away by terrors!
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Like one waking from a dream, so You, O Lord, awaken and despise their form.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 When my heart was grieved and I was pierced within,
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 I was senseless and ignorant; I was a brute beast before You.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Yet I am always with You; You hold my right hand.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 You guide me with Your counsel, and later receive me in glory.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Whom have I in heaven but You? And on earth I desire no one besides You.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 My flesh and my heart may fail, but God is the strength of my heart and my portion forever.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Those far from You will surely perish; You destroy all who are unfaithful to You.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But as for me, it is good to draw near to God. I have made the Lord GOD my refuge, that I may proclaim all Your works.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >