< Psalms 72 >

1 Of Solomon. Endow the king with Your justice, O God, and the son of the king with Your righteousness.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 May he judge Your people with righteousness and Your afflicted with justice.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 May the mountains bring peace to the people, and the hills bring righteousness.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 May he vindicate the afflicted among the people; may he save the children of the needy and crush the oppressor.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 May they fear him as long as the sun shines, as long as the moon remains, through all generations.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 May he be like rain that falls on freshly cut grass, like spring showers that water the earth.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 May the righteous flourish in his days and prosperity abound, until the moon is no more.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 May he rule from sea to sea, and from the Euphrates to the ends of the earth.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 May the nomads bow before him, and his enemies lick the dust.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 May the kings of Tarshish and distant shores bring tribute; may the kings of Sheba and Seba offer gifts.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 May all kings bow down to him and all nations serve him.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 For he will deliver the needy who cry out and the afflicted who have no helper.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 He will take pity on the poor and needy and save the lives of the oppressed.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 He will redeem them from oppression and violence, for their blood is precious in his sight.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Long may he live! May gold from Sheba be given him. May people ever pray for him; may they bless him all day long.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 May there be an abundance of grain in the land; may it sway atop the hills. May its fruit trees flourish like the forests of Lebanon, and its people like the grass of the field.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 May his name endure forever; may his name continue as long as the sun shines. In him may all nations be blessed; may they call him blessed.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Blessed be the LORD God, the God of Israel, who alone does marvelous deeds.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 And blessed be His glorious name forever; may all the earth be filled with His glory. Amen and amen.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Thus conclude the prayers of David son of Jesse.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psalms 72 >