< Psalms 55 >

1 For the choirmaster. With stringed instruments. A Maskil of David. Listen to my prayer, O God, and do not ignore my plea.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Attend to me and answer me. I am restless in my complaint, and distraught
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 at the voice of the enemy, at the pressure of the wicked. For they release disaster upon me and revile me in their anger.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 My heart murmurs within me, and the terrors of death assail me.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Fear and trembling grip me, and horror has overwhelmed me.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 I said, “Oh, that I had wings like a dove! I would fly away and find rest.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 How far away I would flee! In the wilderness I would remain.
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I would hurry to my shelter, far from this raging tempest.”
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 O Lord, confuse and confound their speech, for I see violence and strife in the city.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Day and night they encircle the walls, while malice and trouble lie within.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Destruction is within; oppression and deceit never leave the streets.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 For it is not an enemy who insults me; that I could endure. It is not a foe who rises against me; from him I could hide.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 But it is you, a man like myself, my companion and close friend.
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 We shared sweet fellowship together; we walked with the crowd into the house of God.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Let death seize them by surprise; let them go down to Sheol alive, for evil is with them in their homes. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 But I call to God, and the LORD saves me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Morning, noon, and night, I cry out in distress, and He hears my voice.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 He redeems my soul in peace from the battle waged against me, even though many oppose me.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God will hear and humiliate them— the One enthroned for the ages— (Selah) because they do not change and they have no fear of God.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 My companion attacks his friends; he violates his covenant.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 His speech is smooth as butter, but war is in his heart. His words are softer than oil, yet they are swords unsheathed.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Cast your burden upon the LORD and He will sustain you; He will never let the righteous be shaken.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 But You, O God, will bring them down to the Pit of destruction; men of bloodshed and deceit will not live out half their days. But I will trust in You.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >