< Psalms 31 >
1 For the choirmaster. A Psalm of David. In You, O LORD, I have taken refuge; let me never be put to shame; save me by Your righteousness.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
2 Incline Your ear to me; come quickly to my rescue. Be my rock of refuge, the stronghold of my deliverance.
Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 For You are my rock and my fortress; lead me and guide me for the sake of Your name.
Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 You free me from the net laid out for me, for You are my refuge.
Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
5 Into Your hands I commit my spirit; You have redeemed me, O LORD, God of truth.
Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
6 I hate those who cling to worthless idols, but in the LORD I trust.
Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
7 I will be glad and rejoice in Your loving devotion, for You have seen my affliction; You have known the anguish of my soul.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
8 You have not delivered me to the enemy; You have set my feet in the open.
Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
9 Be merciful to me, O LORD, for I am in distress; my eyes fail from sorrow, my soul and body as well.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
10 For my life is consumed with grief and my years with groaning; my iniquity has drained my strength, and my bones are wasting away.
Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
11 Among all my enemies I am a disgrace, and among my neighbors even more. I am dreaded by my friends— they flee when they see me on the street.
Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
12 I am forgotten like a dead man, out of mind. I am like a broken vessel.
An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
13 For I hear the slander of many; there is terror on every side. They conspire against me and plot to take my life.
Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
14 But I trust in You, O LORD; I say, “You are my God.”
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15 My times are in Your hands; deliver me from my enemies and from those who pursue me.
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16 Make Your face shine on Your servant; save me by Your loving devotion.
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17 O LORD, let me not be ashamed, for I have called on You. Let the wicked be put to shame; let them lie silent in Sheol. (Sheol )
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol )
18 May lying lips be silenced— lips that speak with arrogance against the righteous, full of pride and contempt.
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
19 How great is Your goodness which You have laid up for those who fear You, which You have bestowed before the sons of men on those who take refuge in You!
Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
20 You hide them in the secret place of Your presence from the schemes of men. You conceal them in Your shelter from accusing tongues.
Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
21 Blessed be the LORD, for He has shown me His loving devotion in a city under siege.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
22 In my alarm I said, “I am cut off from Your sight!” But You heard my plea for mercy when I called to You for help.
Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
23 Love the LORD, all His saints. The LORD preserves the faithful, but fully repays the arrogant.
Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
24 Be strong and courageous, all you who hope in the LORD.
Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.