< Psalms 3 >

1 A Psalm of David, when he fled from his son Absalom. O LORD, how my foes have increased! How many rise up against me!
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Many say of me, “God will not deliver him.”
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 But You, O LORD, are a shield around me, my glory, and the One who lifts my head.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 To the LORD I cry aloud, and He answers me from His holy mountain.
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 I lie down and sleep; I wake again, for the LORD sustains me.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 I will not fear the myriads set against me on every side.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Arise, O LORD! Save me, O my God! Strike all my enemies on the jaw; break the teeth of the wicked.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Salvation belongs to the LORD; may Your blessing be on Your people.
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Psalms 3 >