< Psalms 118 >
1 Give thanks to the LORD, for He is good; His loving devotion endures forever.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let Israel say, “His loving devotion endures forever.”
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Let the house of Aaron say, “His loving devotion endures forever.”
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Let those who fear the LORD say, “His loving devotion endures forever.”
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 In my distress I called to the LORD, and He answered and set me free.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 The LORD is on my side; I will not be afraid. What can man do to me?
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 The LORD is on my side; He is my helper. Therefore I will look in triumph on those who hate me.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 It is better to take refuge in the LORD than to trust in man.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 It is better to take refuge in the LORD than to trust in princes.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 All the nations surrounded me, but in the name of the LORD I cut them off.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 They surrounded me on every side, but in the name of the LORD I cut them off.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 They swarmed around me like bees, but they were extinguished like burning thorns; in the name of the LORD I cut them off.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 I was pushed so hard I was falling, but the LORD helped me.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 The LORD is my strength and my song, and He has become my salvation.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 Shouts of joy and salvation resound in the tents of the righteous: “The right hand of the LORD performs with valor!
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 The right hand of the LORD is exalted! The right hand of the LORD performs with valor!”
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 I will not die, but I will live and proclaim what the LORD has done.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 The LORD disciplined me severely, but He has not given me over to death.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Open to me the gates of righteousness, that I may enter and give thanks to the LORD.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 This is the gate of the LORD; the righteous shall enter through it.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 I will give You thanks, for You have answered me, and You have become my salvation.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 The stone the builders rejected has become the cornerstone.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 This is from the LORD, and it is marvelous in our eyes.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 This is the day that the LORD has made; we will rejoice and be glad in it.
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 O LORD, save us, we pray. We beseech You, O LORD, cause us to prosper!
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 Blessed is he who comes in the name of the LORD. From the house of the LORD we bless you.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 The LORD is God; He has made His light to shine upon us. Bind the festal sacrifice with cords to the horns of the altar.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 You are my God, and I will give You thanks. You are my God, and I will exalt You.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Give thanks to the LORD, for He is good; His loving devotion endures forever.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.