< Psalms 110 >

1 A Psalm of David. The LORD said to my Lord: “Sit at My right hand until I make Your enemies a footstool for Your feet.”
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 The LORD extends Your mighty scepter from Zion: “Rule in the midst of Your enemies.”
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Your people shall be willing on Your day of battle. Arrayed in holy splendor, from the womb of the dawn, to You belongs the dew of Your youth.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 The LORD has sworn and will not change His mind: “You are a priest forever in the order of Melchizedek.”
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 The Lord is at Your right hand; He will crush kings in the day of His wrath.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 He will judge the nations, heaping up the dead; He will crush the leaders far and wide.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 He will drink from the brook by the road; therefore He will lift up His head.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< Psalms 110 >