< Psalms 103 >

1 Of David. Bless the LORD, O my soul; all that is within me, bless His holy name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Bless the LORD, O my soul, and do not forget all His kind deeds—
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 He who forgives all your iniquities and heals all your diseases,
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 who redeems your life from the Pit and crowns you with loving devotion and compassion,
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 who satisfies you with good things, so that your youth is renewed like the eagle’s.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 The LORD executes righteousness and justice for all the oppressed.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He made known His ways to Moses, His deeds to the people of Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 The LORD is compassionate and gracious, slow to anger, abounding in loving devotion.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 He will not always accuse us, nor harbor His anger forever.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 He has not dealt with us according to our sins or repaid us according to our iniquities.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as high as the heavens are above the earth, so great is His loving devotion for those who fear Him.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 As far as the east is from the west, so far has He removed our transgressions from us.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 As a father has compassion on his children, so the LORD has compassion on those who fear Him.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For He knows our frame; He is mindful that we are dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 As for man, his days are like grass— he blooms like a flower of the field;
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 when the wind passes over, it vanishes, and its place remembers it no more.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 But from everlasting to everlasting the loving devotion of the LORD extends to those who fear Him, and His righteousness to their children’s children—
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 to those who keep His covenant and remember to obey His precepts.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 The LORD has established His throne in heaven, and His kingdom rules over all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Bless the LORD, all His angels mighty in strength who carry out His word, who hearken to the voice of His command.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Bless the LORD, all His hosts, you servants who do His will.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Bless the LORD, all His works in all places of His dominion. Bless the LORD, O my soul!
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psalms 103 >