< Proverbs 9 >

1 Wisdom has built her house; she has carved out her seven pillars.
Hikima ta gina gidanta; ta yi ginshiƙansa bakwai.
2 She has prepared her meat and mixed her wine; she has also set her table.
Ta shirya abincinta gauraye da ruwan inabinta; ta kuma shirya teburinta.
3 She has sent out her maidservants; she calls out from the heights of the city.
Ta aiki bayinta mata, tana kuma kira daga wurare masu tsayi na birnin.
4 “Whoever is simple, let him turn in here!” she says to him who lacks judgment.
“Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo nan ciki!” Tana faɗa wa marasa hankali.
5 “Come, eat my bread and drink the wine I have mixed.
“Ku zo, ku ci abincina da ruwan inabin da na gauraye.
6 Leave your folly behind, and you will live; walk in the way of understanding.”
Ku bar hanyoyinku marasa hankali za ku kuwa rayu; yi tafiya a hanyar fahimi.
7 He who corrects a mocker brings shame on himself; he who rebukes a wicked man taints himself.
“Duk wanda ya yi wa mai ba’a gyara yana gayyatar zagi duk wanda ya tsawata wa mugu yakan gamu da cin mutunci.
8 Do not rebuke a mocker, or he will hate you; rebuke a wise man, and he will love you.
Kada ka tsawata wa masu ba’a gama za su ƙi ka; ka tsawata wa mai hikima zai kuwa ƙaunace ka.
9 Instruct a wise man, and he will be wiser still; teach a righteous man, and he will increase his learning.
Ka koya wa mai hikima zai kuwa ƙara hikima; ka koya wa mai adalci zai kuwa ƙara koyonsa.
10 The fear of the LORD is the beginning of wisdom, and knowledge of the Holy One is understanding.
“Tsoron Ubangiji shi ne mafarin hikima, sanin Mai Tsarki kuwa fahimi ne.
11 For through wisdom your days will be multiplied, and years will be added to your life.
Gama ta wurina kwanakinka za su yi yawa, za a kuwa ƙara wa ranka shekaru.
12 If you are wise, you are wise to your own advantage; but if you scoff, you alone will bear the consequences.
In kana da hikima, hikimarka za tă ba ka lada; in kai mai ba’a ne, kai kaɗai za ka sha wahala.”
13 The woman named Folly is loud; she is naive and knows nothing.
Wawancin mace a bayyane yake; ba ta da ɗa’a kuma ba ta da sani.
14 She sits at the door of her house, on a seat in the heights of the city,
Takan zauna a ƙofar gidanta, a wurin zama a wurin mafi tsayi na birni,
15 calling out to those who pass by, who make their paths straight.
tana kira ga masu wucewa, waɗanda suke tafiya kai tsaye a hanyarsu.
16 “Whoever is simple, let him turn in here!” she says to him who lacks judgment.
“Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo cikin nan!” Tana ce wa marasa hankali.
17 “Stolen water is sweet, and bread eaten in secret is tasty!”
“Ruwan da aka sata ya fi daɗi; abincin da aka ci a ɓoye ya fi daɗi!”
18 But they do not know that the dead are there, that her guests are in the depths of Sheol. (Sheol h7585)
Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol h7585)

< Proverbs 9 >