< Proverbs 30 >

1 These are the words of Agur son of Jakeh—the burden that this man declared to Ithiel: “I am weary, O God, and worn out.
Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
2 Surely I am the most ignorant of men, and I lack the understanding of a man.
“Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
3 I have not learned wisdom, and I have no knowledge of the Holy One.
Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
4 Who has ascended to heaven and come down? Who has gathered the wind in His hands? Who has bound up the waters in His cloak? Who has established all the ends of the earth? What is His name, and what is the name of His Son— surely you know!
Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
5 Every word of God is flawless; He is a shield to those who take refuge in Him.
“Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
6 Do not add to His words, lest He rebuke you and prove you a liar.
Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
7 Two things I ask of You— do not refuse me before I die:
“Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
8 Keep falsehood and deceitful words far from me. Give me neither poverty nor riches; feed me with the bread that is my portion.
Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
9 Otherwise, I may have too much and deny You, saying, ‘Who is the LORD?’ Or I may become poor and steal, profaning the name of my God.
In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
10 Do not slander a servant to his master, or he will curse you, and you will bear the guilt.
“Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
11 There is a generation of those who curse their fathers and do not bless their mothers.
“Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
12 There is a generation of those who are pure in their own eyes and yet unwashed of their filth.
waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
13 There is a generation—how haughty are their eyes and pretentious are their glances—
waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
14 there is a generation whose teeth are swords and whose jaws are knives, devouring the oppressed from the earth and the needy from among men.
waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
15 The leech has two daughters: Give and Give. There are three things that are never satisfied, four that never say, ‘Enough!’:
“Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
16 Sheol, the barren womb, land never satisfied with water, and fire that never says, ‘Enough!’ (Sheol h7585)
Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
17 As for the eye that mocks a father and scorns obedience to a mother, may the ravens of the valley pluck it out and young vultures devour it.
“Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
18 There are three things too wonderful for me, four that I cannot understand:
“Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
19 the way of an eagle in the sky, the way of a snake on a rock, the way of a ship at sea, and the way of a man with a maiden.
yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
20 This is the way of an adulteress: She eats and wipes her mouth and says, ‘I have done nothing wrong.’
“Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
21 Under three things the earth trembles, under four it cannot bear up:
“Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
22 a servant who becomes king, a fool who is filled with food,
bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
23 an unloved woman who marries, and a maidservant who supplants her mistress.
macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
24 Four things on earth are small, yet they are exceedingly wise:
“Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
25 The ants are creatures of little strength, yet they store up their food in the summer;
Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
26 the rock badgers are creatures of little power, yet they make their homes in the rocks;
remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
27 the locusts have no king, yet they all advance in formation;
fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
28 and the lizard can be caught in one’s hands, yet it is found in the palaces of kings.
ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
29 There are three things that are stately in their stride, and four that are impressive in their walk:
“Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
30 a lion, mighty among beasts, refusing to retreat before anything;
zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
31 a strutting rooster; a he-goat; and a king with his army around him.
zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
32 If you have foolishly exalted yourself or if you have plotted evil, put your hand over your mouth.
“In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
33 For as the churning of milk yields butter, and the twisting of the nose draws blood, so the stirring of anger brings forth strife.”
Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”

< Proverbs 30 >