< Numbers 3 >

1 This is the account of Aaron and Moses at the time the LORD spoke with Moses on Mount Sinai.
Waɗannan su ne zuriyar Haruna da Musa a lokacin da Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai.
2 These are the names of the sons of Aaron: Nadab the firstborn, then Abihu, Eleazar, and Ithamar.
Sunayen’ya’yan Haruna su ne, Nadab ɗan fari, da Abihu, da Eleyazar da Itamar.
3 These were Aaron’s sons, the anointed priests, who were ordained to serve as priests.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Haruna, shafaffun firistocin da aka naɗa domin su yi aiki firist.
4 Nadab and Abihu, however, died in the presence of the LORD when they offered unauthorized fire before the LORD in the Wilderness of Sinai. And since they had no sons, only Eleazar and Ithamar served as priests during the lifetime of their father Aaron.
Amma Nadab da Abihu suka fāɗi suka mutu a gaban Ubangiji a Hamadar Sinai a sa’ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta a gabansa. Ba su kuwa da’ya’ya; saboda haka Eleyazar da Itamar kaɗai suka yi aiki firist a zamanin mahaifinsu Haruna.
5 Then the LORD said to Moses,
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 “Bring the tribe of Levi and present them to Aaron the priest to assist him.
“Ka kawo mutanen Lawi, ka kuma gabatar da su ga Haruna firist, don su taya shi aiki.
7 They are to perform duties for him and for the whole congregation before the Tent of Meeting, attending to the service of the tabernacle.
Za su yi wa Haruna da dukan al’umma aikace-aikace a Tentin Sujada, ta wurin yin aikin tabanakul.
8 They shall take care of all the furnishings of the Tent of Meeting and fulfill obligations for the Israelites by attending to the service of the tabernacle.
Za su lura da dukan kayayyakin Tentin Sujada, suna cika hakkin Isra’ilawa ta wurin yin aiki a tabanakul.
9 Assign the Levites to Aaron and his sons; they have been given exclusively to him from among the Israelites.
Ka ba da Lawiyawa ga Haruna da’ya’yansa; su ne za su zama Isra’ilawan da za a ba da su ɗungum gare shi.
10 So you shall appoint Aaron and his sons to carry out the duties of the priesthood; but any outsider who approaches the tabernacle must be put to death.”
Ka naɗa Haruna da’ya’yansa su yi aiki firistoci; duk wanda ya yi shisshigi a wuri mai tsarki kuwa dole a kashe shi.”
11 Again the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
12 “Behold, I have taken the Levites from among the children of Israel in place of every firstborn Israelite from the womb. The Levites belong to Me,
“Ga shi na ɗauki Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a maimakon ɗan fari na kowace mace a Isra’ila. Lawiyawa nawa ne,
13 for all the firstborn are Mine. On the day I struck down every firstborn in the land of Egypt, I consecrated to Myself all the firstborn in Israel, both man and beast. They are Mine; I am the LORD.”
gama duk’ya’yan fari nawa ne. Lokacin da karkashe duk’ya’yan fari a Masar, na keɓe wa kaina kowane ɗan fari a Isra’ila, ko mutum, ko dabba. Za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.”
14 Then the LORD spoke to Moses in the Wilderness of Sinai, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai ya ce,
15 “Number the Levites by their families and clans. You are to count every male a month old or more.”
“Ka ƙidaya Lawiyawa bisa ga iyalansu da kabilarsu. Ka ƙidaya kowane ɗan jinjiri mai wata ɗaya ko fiye.”
16 So Moses numbered them according to the word of the LORD, as he had been commanded.
Saboda haka Musa ya ƙidaya su duka, kamar yadda maganar Ubangiji ta umarta.
17 These were the sons of Levi by name: Gershon, Kohath, and Merari.
Ga sunayen’ya’yan Lawi, Gershon, Kohat da Merari.
18 These were the names of the sons of Gershon by their clans: Libni and Shimei.
Ga sunayen mutanen Gershon, Libni, da Shimeyi
19 The sons of Kohath by their clans were Amram, Izhar, Hebron, and Uzziel.
Sunayen mutanen Kohat kuwa su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.
20 And the sons of Merari by their clans were Mahli and Mushi. These were the clans of the Levites, according to their families.
Dangin Merari su ne. Mali da Mushi. Ga kabilan Lawiyawa bisa ga iyalansu.
21 From Gershon came the Libnite clan and the Shimeite clan; these were the Gershonite clans.
A wajen Gershonawa, kabilarsa su ne Libniyawa, da Shimeyiyawa; waɗannan su ne mutanen Gershom.
22 The number of all the males a month old or more was 7,500.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya zuwa gaba da haihuwa su kai 7,500.
23 The Gershonite clans were to camp on the west, behind the tabernacle,
Kabilar Gershonawa za su yi sansani ta fuskar yamma, a bayan tabanakul.
24 and the leader of the families of the Gershonites was Eliasaph son of Lael.
Eliyasaf ɗan Layel shi ne shugaban iyalan Gershonawa.
25 The duties of the Gershonites at the Tent of Meeting were the tabernacle and tent, its covering, the curtain for the entrance to the Tent of Meeting,
A Tentin Sujada, Gershonawa su ne za su lura da mazauni da tabanakul da kuma tentin, abubuwan rufensa, labule a ƙofar Tentin Sujada,
26 the curtains of the courtyard, the curtain for the entrance to the courtyard that surrounds the tabernacle and altar, and the cords—all the service for these items.
da labulen filin da yake kewaye da tabanakul da kuma bagade, da igiyoyi, da kuma kowane abin da ya danganci aikinsu.
27 From Kohath came the clans of the Amramites, the Izharites, the Hebronites, and the Uzzielites; these were the clans of the Kohathites.
Kabilar Kohat su ne, Amramawa da Izharawa da Hebronawa da Uzziyelawa; waɗannan su ne kabilar Kohatawa.
28 The number of all the males a month old or more was 8,600. They were responsible for the duties of the sanctuary.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 8,600 ne. Kohatawa ne suke lura da wuri mai tsarki.
29 The clans of the Kohathites were to camp on the south side of the tabernacle,
Kohatawa za su yi sansani a kudu da tabanakul.
30 and the leader of the families of the Kohathites was Elizaphan son of Uzziel.
Shugaban kabilar Kohatawa shi ne Elizafan ɗan Uzziyel.
31 Their duties were the ark, the table, the lampstand, the altars, the articles of the sanctuary used with them, and the curtain—all the service for these items.
Su ne da hakkin kula da akwatin alkawari, tebur, wurin ajiye fitila, bagade, kayayyakin wuri mai tsarki da ake amfani da su a sujada, labule, da kuma kome da ya danganci aikinsu.
32 The chief of the leaders of the Levites was Eleazar son of Aaron the priest; he oversaw those responsible for the duties of the sanctuary.
Babban shugaban Lawiyawa shi ne Eleyazar ɗan Haruna, firist. An naɗa shi a kan waɗanda suke kula da wuri mai tsarki.
33 From Merari came the clans of the Mahlites and Mushites; these were the Merarite clans.
Kabilar Merari su ne Maliyawa da Mushiyawa; waɗannan su ne kabilar Merari.
34 The number of all the males a month old or more was 6,200.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 6,200 ne.
35 The leader of the families of the Merarites was Zuriel son of Abihail; they were to camp on the north side of the tabernacle.
Shugaban iyalan Merari shi ne Zuriyel ɗan Abihayil. Za su yi sansani arewa da tabanakul.
36 The duties assigned to the sons of Merari were the tabernacle’s frames, crossbars, posts, bases, and all its equipment—all the service for these items,
Kabilar Merari ne aka sa su lura da katakan tabanakul, sandunanta, dogayen sandunanta, tarukanta, dukan kayan aiki da kowane abin da ya danganci aikinsu,
37 as well as the posts of the surrounding courtyard with their bases, tent pegs, and ropes.
da ginshiƙai kewaye da filin tare da rammuka da turaku da igiyoyinsu.
38 Moses, Aaron, and Aaron’s sons were to camp to the east of the tabernacle, toward the sunrise, before the Tent of Meeting. They were to perform the duties of the sanctuary as a service on behalf of the Israelites; but any outsider who approached the sanctuary was to be put to death.
Musa da Haruna da’ya’yansu za su yi sansani gabas da tabanakul, wajen fitowar rana; a gaban Tentin Sujada. Su ne da hakkin lura da wuri mai tsarki a madadin Isra’ilawa. Duk wani wanda ba ya wannan aiki, ya kuma kusaci wuri mai tsarki, za a kashe shi.
39 The total number of Levites that Moses and Aaron counted by their clans at the LORD’s command, including all the males a month old or more, was 22,000.
Jimillar Lawiyawan da Musa da Haruna suka ƙidaya bisa ga umarnin Ubangiji bisa ga danginsu, haɗe da kowane jariri daga wata ɗaya ko fiye, 22,000 ne.
40 Then the LORD said to Moses, “Number every firstborn male of the Israelites a month old or more, and list their names.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ƙidaya dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa maza daga wata ɗaya da kuma fiye ka kuma rubuta sunayensu.
41 You are to take the Levites for Me—I am the LORD—in place of all the firstborn of Israel, and the livestock of the Levites in place of all the firstborn of the livestock of the Israelites.”
Ka ɗauko mini Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa, haka ma na dabbobi na Lawiyawa, a maimakon’ya’yan fari na dabbobin Isra’ilawa. Ni ne Ubangiji.”
42 So Moses numbered all the firstborn of the Israelites, as the LORD had commanded him.
Haka Musa ya ƙidaya’ya’yan fari na Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
43 The total number of the firstborn males a month old or more, listed by name, was 22,273.
Jimillar’ya’yan fari maza daga wata ɗaya da kuma fiye, da aka rubuta bisa ga sunayensu, 22,273 ne.
44 Again the LORD spoke to Moses, saying,
Sai Ubangiji ya kuma yi magana da Musa ya ce,
45 “Take the Levites in place of all the firstborn of Israel, and the livestock of the Levites in place of their livestock. The Levites belong to Me; I am the LORD.
“Ka ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ila, dabbobin Lawiyawa kuma a maimakon dabbobinsu. Lawiyawa za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.
46 To redeem the 273 firstborn Israelites who outnumber the Levites,
Don a fanshi’ya’yan fari 273 na Isra’ilawa da suka fi Lawiyawa yawa,
47 you are to collect five shekels for each one, according to the sanctuary shekel of twenty gerahs.
ka karɓi shekel biyar domin kowannensu, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, wanda yake da nauyin gera ashirin.
48 Give the money to Aaron and his sons as the redemption price for the excess among the Israelites.”
Ka ba wa Haruna da’ya’yansa kuɗin fansar da ya haura kai na’ya’yan farin Isra’ilawa.”
49 So Moses collected the redemption money from those in excess of the number redeemed by the Levites.
Haka, Musa ya karɓi kuɗin fansar waɗanda suka haura yawan Lawiyawa.
50 He collected the money from the firstborn of the Israelites: 1,365 shekels, according to the sanctuary shekel.
Daga’ya’yan fari na Isra’ilawa, ya karɓi azurfa masu nauyin shekel 1,365, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri.
51 And Moses gave the redemption money to Aaron and his sons in obedience to the word of the LORD, just as the LORD had commanded him.
Sa’an nan Musa ya ba da kuɗin fansar ga Haruna da’ya’yansa, yadda maganar Ubangiji ta umarce shi.

< Numbers 3 >