< Matthew 25 >
1 “At that time the kingdom of heaven will be like ten virgins who took their lamps and went out to meet the bridegroom.
“A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
2 Five of them were foolish, and five were wise.
Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
3 The foolish ones took their lamps but did not take along any extra oil.
Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
4 But the wise ones took oil in flasks along with their lamps.
Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
5 When the bridegroom was delayed, they all became drowsy and fell asleep.
Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
6 At midnight the cry rang out: ‘Here is the bridegroom! Come out to meet him!’
“Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
7 Then all the virgins woke up and trimmed their lamps.
“Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
8 The foolish ones said to the wise, ‘Give us some of your oil; our lamps are going out.’
Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
9 ‘No,’ said the wise ones, ‘or there may not be enough for both us and you. Instead, go to those who sell oil and buy some for yourselves.’
“Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
10 But while they were on their way to buy it, the bridegroom arrived. Those who were ready went in with him to the wedding banquet, and the door was shut.
“Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
11 Later the other virgins arrived and said, ‘Lord, lord, open the door for us!’
“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
12 But he replied, ‘Truly I tell you, I do not know you.’
“Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
13 Therefore keep watch, because you do not know the day or the hour.
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.
14 For it is just like a man going on a journey, who called his servants and entrusted them with his possessions.
“Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa.
15 To one he gave five talents, to another two talents, and to another one talent—each according to his own ability. And he went on his journey.
Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa.
16 The servant who had received the five talents went at once and put them to work and gained five more.
Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar.
17 Likewise, the one with the two talents gained two more.
Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu.
18 But the servant who had received the one talent went off, dug a hole in the ground, and hid his master’s money.
Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.
19 After a long time the master of those servants returned to settle accounts with them.
“Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su.
20 The servant who had received the five talents came and presented five more. ‘Master,’ he said, ‘you entrusted me with five talents. See, I have gained five more.’
Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’
21 His master replied, ‘Well done, good and faithful servant! You have been faithful with a few things; I will put you in charge of many things. Enter into the joy of your master!’
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
22 The servant who had received the two talents also came and said, ‘Master, you entrusted me with two talents. See, I have gained two more.’
“Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’
23 His master replied, ‘Well done, good and faithful servant! You have been faithful with a few things; I will put you in charge of many things. Enter into the joy of your master!’
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
24 Finally, the servant who had received the one talent came and said, ‘Master, I knew that you are a hard man, reaping where you have not sown and gathering where you have not scattered seed.
“Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba.
25 So I was afraid and went out and hid your talent in the ground. See, you have what belongs to you.’
Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’
26 ‘You wicked, lazy servant!’ replied his master. ‘You knew that I reap where I have not sown and gather where I have not scattered seed.
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba?
27 Then you should have deposited my money with the bankers, and on my return I would have received it back with interest.
To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.
28 Therefore take the talent from him and give it to the one who has ten talents.
“‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma.
29 For everyone who has will be given more, and he will have an abundance. But the one who does not have, even what he has will be taken away from him.
Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.
30 And throw that worthless servant into the outer darkness, where there will be weeping and gnashing of teeth.’
Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
31 When the Son of Man comes in His glory, and all the angels with Him, He will sit on His glorious throne.
“Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama.
32 All the nations will be gathered before Him, and He will separate the people one from another, as a shepherd separates the sheep from the goats.
Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki.
33 He will place the sheep on His right and the goats on His left.
Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.
34 Then the King will say to those on His right, ‘Come, you who are blessed by My Father, inherit the kingdom prepared for you from the foundation of the world.
“Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya.
35 For I was hungry and you gave Me something to eat, I was thirsty and you gave Me something to drink, I was a stranger and you took Me in,
Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni,
36 I was naked and you clothed Me, I was sick and you looked after Me, I was in prison and you visited Me.’
da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’
37 Then the righteous will answer Him, ‘Lord, when did we see You hungry and feed You, or thirsty and give You something to drink?
“Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha?
38 When did we see You a stranger and take You in, or naked and clothe You?
Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura?
39 When did we see You sick or in prison and visit You?’
Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’
40 And the King will reply, ‘Truly I tell you, whatever you did for one of the least of these brothers of Mine, you did for Me.’
“Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’
41 Then He will say to those on His left, ‘Depart from Me, you who are cursed, into the eternal fire prepared for the devil and his angels. (aiōnios )
“Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios )
42 For I was hungry and you gave Me nothing to eat, I was thirsty and you gave Me nothing to drink,
Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba,
43 I was a stranger and you did not take Me in, I was naked and you did not clothe Me, I was sick and in prison and you did not visit Me.’
da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’
44 And they too will reply, ‘Lord, when did we see You hungry or thirsty or a stranger or naked or sick or in prison, and did not minister to You?’
“Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’
45 Then the King will answer, ‘Truly I tell you, whatever you did not do for one of the least of these, you did not do for Me.’
“Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’
46 And they will go away into eternal punishment, but the righteous into eternal life.” (aiōnios )
“Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios )