< Mark 1 >

1 This is the beginning of the gospel of Jesus Christ, the Son of God.
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 As it is written in Isaiah the prophet: “Behold, I will send My messenger ahead of You, who will prepare Your way.”
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 “A voice of one calling in the wilderness, ‘Prepare the way for the Lord, make straight paths for Him.’”
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 John the Baptist appeared in the wilderness, preaching a baptism of repentance for the forgiveness of sins.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 People went out to him from all of Jerusalem and the countryside of Judea. Confessing their sins, they were baptized by him in the Jordan River.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 John was clothed in camel’s hair, with a leather belt around his waist. His food was locusts and wild honey.
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 And he began to proclaim: “After me will come One more powerful than I, the straps of whose sandals I am not worthy to stoop down and untie.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 I baptize you with water, but He will baptize you with the Holy Spirit.”
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 In those days Jesus came from Nazareth in Galilee and was baptized by John in the Jordan.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 As soon as Jesus came up out of the water, He saw the heavens breaking open and the Spirit descending on Him like a dove.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 And a voice came from heaven: “You are My beloved Son; in You I am well pleased.”
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 At once the Spirit drove Jesus into the wilderness,
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 and He was there for forty days, being tempted by Satan. He was with the wild animals, and the angels ministered to Him.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 After the arrest of John, Jesus went into Galilee and proclaimed the gospel of God.
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 “The time is fulfilled,” He said, “and the kingdom of God is near. Repent and believe in the gospel!”
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 As Jesus was walking beside the Sea of Galilee, He saw Simon and his brother Andrew. They were casting a net into the sea, for they were fishermen.
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 “Come, follow Me,” Jesus said, “and I will make you fishers of men.”
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 And at once they left their nets and followed Him.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 Going on a little farther, He saw James son of Zebedee and his brother John. They were in a boat, mending their nets.
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 Immediately Jesus called them, and they left their father Zebedee in the boat with the hired men and followed Him.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 Then Jesus and His companions went to Capernaum, and right away Jesus entered the synagogue on the Sabbath and began to teach.
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 The people were astonished at His teaching, because He taught as one who had authority, and not as the scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 Suddenly a man with an unclean spirit cried out in the synagogue:
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 “What do You want with us, Jesus of Nazareth? Have You come to destroy us? I know who You are—the Holy One of God!”
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 But Jesus rebuked the spirit. “Be silent!” He said. “Come out of him!”
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 At this, the unclean spirit threw the man into convulsions and came out with a loud shriek.
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 All the people were amazed and began to ask one another, “What is this? A new teaching with authority! He commands even the unclean spirits, and they obey Him!”
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 And the news about Jesus spread quickly through the whole region of Galilee.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 As soon as Jesus and His companions had left the synagogue, they went with James and John to the home of Simon and Andrew.
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 Simon’s mother-in-law was sick in bed with a fever, and they promptly told Jesus about her.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 So He went to her, took her by the hand, and helped her up. The fever left her, and she began to serve them.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 That evening, after sunset, people brought to Jesus all who were sick and demon-possessed,
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 and the whole town gathered at the door.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 And He healed many who were ill with various diseases and drove out many demons. But He would not allow the demons to speak, because they knew who He was.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 Early in the morning, while it was still dark, Jesus got up and slipped out to a solitary place to pray.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 Simon and his companions went to look for Him,
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 and when they found Him, they said, “Everyone is looking for You!”
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 But Jesus answered, “Let us go on to the neighboring towns so I can preach there as well, for that is why I have come.”
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 So He went throughout Galilee, preaching in their synagogues and driving out demons.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 Then a leper came to Jesus, begging on his knees: “If You are willing, You can make me clean.”
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 Moved with compassion, Jesus reached out His hand and touched the man. “I am willing,” He said. “Be clean!”
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 And immediately the leprosy left him, and the man was cleansed.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 Jesus promptly sent him away with a stern warning:
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 “See that you don’t tell anyone. But go, show yourself to the priest and present the offering Moses prescribed for your cleansing, as a testimony to them.”
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 But the man went out and openly began to proclaim and spread the news. Consequently, Jesus could no longer enter a town in plain view, but He stayed out in solitary places. Yet people came to Him from every quarter.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< Mark 1 >