< Luke 22 >
1 Now the Feast of Unleavened Bread, called the Passover, was approaching,
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 and the chief priests and scribes were looking for a way to put Jesus to death; for they feared the people.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 Then Satan entered Judas Iscariot, who was one of the Twelve.
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 And Judas went to discuss with the chief priests and temple officers how he might betray Jesus to them.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 They were delighted and agreed to give him money.
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 Judas consented, and began to look for an opportunity to betray Jesus to them in the absence of a crowd.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Then came the day of Unleavened Bread on which the Passover lamb was to be sacrificed.
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 Jesus sent Peter and John, saying, “Go and prepare for us to eat the Passover.”
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 “Where do You want us to prepare it?” they asked.
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 He answered, “When you enter the city, a man carrying a jug of water will meet you. Follow him to the house he enters,
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 and say to the owner of that house, ‘The Teacher asks: Where is the guest room, where I may eat the Passover with My disciples?’
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 And he will show you a large upper room, already furnished. Make preparations there.”
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 So they went and found it just as Jesus had told them. And they prepared the Passover.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 When the hour had come, Jesus reclined at the table with His apostles.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 And He said to them, “I have eagerly desired to eat this Passover with you before My suffering.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 For I tell you that I will not eat it again until it is fulfilled in the kingdom of God.”
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 After taking the cup, He gave thanks and said, “Take this and divide it among yourselves.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 For I tell you that I will not drink of the fruit of the vine from now on until the kingdom of God comes.”
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 And He took the bread, gave thanks and broke it, and gave it to them, saying, “This is My body, given for you; do this in remembrance of Me.”
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 In the same way, after supper He took the cup, saying, “This cup is the new covenant in My blood, which is poured out for you.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 Look! The hand of My betrayer is with Mine on the table.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 Indeed, the Son of Man will go as it has been determined, but woe to that man who betrays Him.”
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 Then they began to question among themselves which of them was going to do this.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 A dispute also arose among the disciples as to which of them would be considered the greatest.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 So Jesus declared, “The kings of the Gentiles lord it over them, and those in authority over them call themselves benefactors.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 But you shall not be like them. Instead, the greatest among you should be like the youngest, and the one who leads like the one who serves.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 For who is greater, the one who reclines at the table or the one who serves? Is it not the one who reclines? But I am among you as one who serves.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 You are the ones who have stood by Me in My trials.
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 And I bestow on you a kingdom, just as My Father has bestowed one on Me,
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 so that you may eat and drink at My table in My kingdom, and sit on thrones, judging the twelve tribes of Israel.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 Simon, Simon, Satan has asked to sift each of you like wheat.
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 But I have prayed for you, Simon, that your faith will not fail. And when you have turned back, strengthen your brothers.”
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 “Lord,” said Peter, “I am ready to go with You even to prison and to death.”
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 But Jesus replied, “I tell you, Peter, the rooster will not crow today until you have denied three times that you know Me.”
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Then Jesus asked them, “When I sent you out without purse or bag or sandals, did you lack anything?” “Nothing,” they answered.
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 “Now, however,” He told them, “the one with a purse should take it, and likewise a bag; and the one without a sword should sell his cloak and buy one.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 For I tell you that this Scripture must be fulfilled in Me: ‘And He was numbered with the transgressors.’ For what is written about Me is reaching its fulfillment.”
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 So they said, “Look, Lord, here are two swords.” “That is enough,” He answered.
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 Jesus went out as usual to the Mount of Olives, and the disciples followed Him.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 When He came to the place, He told them, “Pray that you will not enter into temptation.”
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 And He withdrew about a stone’s throw beyond them, where He knelt down and prayed,
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 “Father, if You are willing, take this cup from Me. Yet not My will, but Yours be done.”
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 Then an angel from heaven appeared to Him and strengthened Him.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 And in His anguish, He prayed more earnestly, and His sweat became like drops of blood falling to the ground.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 When Jesus rose from prayer and returned to the disciples, He found them asleep, exhausted from sorrow.
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 “Why are you sleeping?” He asked. “Get up and pray so that you will not enter into temptation.”
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 While He was still speaking, a crowd arrived, led by the man called Judas, one of the Twelve. He approached Jesus to kiss Him.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 But Jesus asked him, “Judas, are you betraying the Son of Man with a kiss?”
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 Those around Jesus saw what was about to happen and said, “Lord, should we strike with our swords?”
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 And one of them struck the servant of the high priest, cutting off his right ear.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 But Jesus answered, “No more of this!” And He touched the man’s ear and healed him.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Then Jesus said to the chief priests, temple officers, and elders who had come for Him, “Have you come out with swords and clubs as you would against an outlaw?
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 Every day I was with you in the temple courts, and you did not lay a hand on Me. But this hour belongs to you and to the power of darkness.”
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 Then they seized Jesus, led Him away, and took Him into the house of the high priest. And Peter followed at a distance.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 When those present had kindled a fire in the middle of the courtyard and sat down together, Peter sat down among them.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 A servant girl saw him seated in the firelight and looked intently at him. “This man also was with Him,” she said.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But Peter denied it. “Woman, I do not know Him,” he said.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 A short time later, someone else saw him and said, “You also are one of them.” But Peter said, “Man, I am not.”
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 About an hour later, another man insisted, “Certainly this man was with Him, for he too is a Galilean.”
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 “Man, I do not know what you are talking about,” Peter replied. While he was still speaking, the rooster crowed.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 And the Lord turned and looked at Peter. Then Peter remembered the word that the Lord had spoken to him: “Before the rooster crows today, you will deny Me three times.”
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 And he went outside and wept bitterly.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 The men who were holding Jesus began to mock Him and beat Him.
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 They blindfolded Him and kept demanding, “Prophesy! Who hit You?”
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 And they said many other blasphemous things against Him.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 At daybreak the council of the elders of the people, both the chief priests and scribes, met together. They led Jesus into their Sanhedrin and said,
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 “If You are the Christ, tell us.” Jesus answered, “If I tell you, you will not believe.
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 And if I ask you a question, you will not answer.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 But from now on the Son of Man will be seated at the right hand of the power of God.”
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 So they all asked, “Are You then the Son of God?” He replied, “You say that I am.”
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 “Why do we need any more testimony?” they declared. “We have heard it for ourselves from His own lips.”
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”