< Luke 17 >
1 Jesus said to His disciples, “It is inevitable that stumbling blocks will come, but woe to the one through whom they come!
Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
2 It would be better for him to have a millstone hung around his neck and to be thrown into the sea than to cause one of these little ones to stumble.
Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
3 Watch yourselves. If your brother sins, rebuke him; and if he repents, forgive him.
Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
4 Even if he sins against you seven times in a day, and seven times returns to say, ‘I repent,’ you must forgive him.”
In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
5 The apostles said to the Lord, “Increase our faith!”
Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
6 And the Lord answered, “If you have faith the size of a mustard seed, you can say to this mulberry tree, ‘Be uprooted and planted in the sea,’ and it will obey you.
Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
7 Which of you whose servant comes in from plowing or shepherding in the field will say to him, ‘Come at once and sit down to eat’?
“In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
8 Instead, won’t he tell him, ‘Prepare my meal and dress yourself to serve me while I eat and drink; and afterward you may eat and drink’?
Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
9 Does he thank the servant because he did what he was told?
Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
10 So you also, when you have done everything commanded of you, should say, ‘We are unworthy servants; we have only done our duty.’”
Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
11 While Jesus was on His way to Jerusalem, He was passing between Samaria and Galilee.
Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
12 As He entered one of the villages, He was met by ten lepers. They stood at a distance
Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
13 and raised their voices, shouting, “Jesus, Master, have mercy on us!”
suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
14 When Jesus saw them, He said, “Go, show yourselves to the priests.” And as they were on their way, they were cleansed.
Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
15 When one of them saw that he was healed, he came back, praising God in a loud voice.
Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
16 He fell facedown at Jesus’ feet in thanksgiving to Him—and he was a Samaritan.
Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
17 “Were not all ten cleansed?” Jesus asked. “Where then are the other nine?
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
18 Was no one found except this foreigner to return and give glory to God?”
Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
19 Then Jesus said to him, “Rise and go; your faith has made you well!”
Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 When asked by the Pharisees when the kingdom of God would come, Jesus replied, “The kingdom of God will not come with observable signs.
Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
21 Nor will people say, ‘Look, here it is,’ or ‘There it is.’ For you see, the kingdom of God is in your midst.”
Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
22 Then He said to the disciples, “The time is coming when you will long to see one of the days of the Son of Man, but you will not see it.
Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
23 People will tell you, ‘Look, there He is!’ or ‘Look, here He is!’ Do not go out or chase after them.
Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
24 For just as the lightning flashes and lights up the sky from one end to the other, so will be the Son of Man in His day.
Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
25 But first He must suffer many things and be rejected by this generation.
Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
26 Just as it was in the days of Noah, so also will it be in the days of the Son of Man:
“Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
27 People were eating and drinking, marrying and being given in marriage, up to the day Noah entered the ark. Then the flood came and destroyed them all.
Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
28 It was the same in the days of Lot: People were eating and drinking, buying and selling, planting and building.
“Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
29 But on the day Lot left Sodom, fire and sulfur rained down from heaven and destroyed them all.
Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
30 It will be just like that on the day the Son of Man is revealed.
“Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
31 On that day, let no one on the housetop come down to retrieve his possessions. Likewise, let no one in the field return for anything he has left behind.
A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
33 Whoever tries to save his life will lose it, but whoever loses his life will preserve it.
Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
34 I tell you, on that night two people will be in one bed: One will be taken and the other left.
Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
35 Two women will be grinding grain together: One will be taken and the other left.”
Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
37 “Where, Lord?” they asked. Jesus answered, “Wherever there is a carcass, there the vultures will gather.”
Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”