< Lamentations 3 >

1 I am the man who has seen affliction under the rod of God’s wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He has driven me away and made me walk in darkness instead of light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Indeed, He keeps turning His hand against me all day long.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He has worn away my flesh and skin; He has shattered my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He has besieged me and surrounded me with bitterness and hardship.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He has made me dwell in darkness like those dead for ages.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He has walled me in so I cannot escape; He has weighed me down with chains.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Even when I cry out and plead for help, He shuts out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He has barred my ways with cut stones; He has made my paths crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He is a bear lying in wait, a lion hiding in ambush.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He forced me off my path and tore me to pieces; He left me without help.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He bent His bow and set me as the target for His arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He pierced my kidneys with His arrows.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I am a laughingstock to all my people; they mock me in song all day long.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He has filled me with bitterness; He has intoxicated me with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 He has ground my teeth with gravel and trampled me in the dust.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 My soul has been deprived of peace; I have forgotten what prosperity is.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 So I say, “My strength has perished, along with my hope from the LORD.”
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember my affliction and wandering, the wormwood and the gall.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Surely my soul remembers and is humbled within me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Yet I call this to mind, and therefore I have hope:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Because of the loving devotion of the LORD we are not consumed, for His mercies never fail.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 They are new every morning; great is Your faithfulness!
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 “The LORD is my portion,” says my soul, “therefore I will hope in Him.”
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 The LORD is good to those who wait for Him, to the soul who seeks Him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 It is good to wait quietly for the salvation of the LORD.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 It is good for a man to bear the yoke while he is still young.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Let him sit alone in silence, for God has disciplined him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Let him bury his face in the dust— perhaps there is still hope.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Let him offer his cheek to the one who would strike him; let him be filled with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord will not cast us off forever.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Even if He causes grief, He will show compassion according to His abundant loving devotion.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 For He does not willingly afflict or grieve the sons of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush underfoot all the prisoners of the land,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 to deny a man justice before the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 to subvert a man in his lawsuit— of these the Lord does not approve.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who has spoken and it came to pass, unless the Lord has ordained it?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Do not both adversity and good come from the mouth of the Most High?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Why should any mortal man complain, in view of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us examine and test our ways, and turn back to the LORD.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our hearts and hands to God in heaven:
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 “We have sinned and rebelled; You have not forgiven.”
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 You have covered Yourself in anger and pursued us; You have killed without pity.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have covered Yourself with a cloud that no prayer can pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 You have made us scum and refuse among the nations.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies open their mouths against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Panic and pitfall have come upon us— devastation and destruction.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Streams of tears flow from my eyes over the destruction of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 My eyes overflow unceasingly, without relief,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 until the LORD looks down from heaven and sees.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 My eyes bring grief to my soul because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Without cause my enemies hunted me like a bird.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They dropped me alive into a pit and cast stones upon me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 The waters flowed over my head, and I thought I was going to die.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called on Your name, O LORD, out of the depths of the Pit.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 You heard my plea: “Do not ignore my cry for relief.”
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 You drew near when I called on You; You said, “Do not be afraid.”
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 You defend my cause, O Lord; You redeem my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 You have seen, O LORD, the wrong done to me; vindicate my cause!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You have seen all their malice, all their plots against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 O LORD, You have heard their insults, all their plots against me—
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 the slander and murmuring of my assailants against me all day long.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 When they sit and when they rise, see how they mock me in song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 You will pay them back what they deserve, O LORD, according to the work of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Put a veil of anguish over their hearts; may Your curse be upon them!
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 You will pursue them in anger and exterminate them from under Your heavens, O LORD.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >