< John 15 >
1 “I am the true vine, and My Father is the keeper of the vineyard.
“Ni ne kuringar inabi na gaskiya, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 He cuts off every branch in Me that bears no fruit, and every branch that does bear fruit, He prunes to make it even more fruitful.
Yakan sare kowane reshe a cikina da ba ya’ya’ya, amma yakan ƙundume kowane reshe da yake ba da’ya’ya, domin yă ƙara ba da’ya’ya.
3 You are already clean because of the word I have spoken to you.
Kun riga kun zama masu tsabta saboda maganar da na yi muku.
4 Remain in Me, and I will remain in you. Just as no branch can bear fruit by itself unless it remains in the vine, neither can you bear fruit unless you remain in Me.
Ku kasance a cikina, ni kuma zan kasance a cikinku. Babu reshen da zai iya yin’ya’ya da kansa, dole yă kasance a jikin kuringar inabin. Haka ku ma, ba za ku iya ba da’ya’ya ba sai kun kasance a cikina.
5 I am the vine and you are the branches. The one who remains in Me, and I in him, will bear much fruit. For apart from Me you can do nothing.
“Ni ne kuringar inabin; ku ne kuma rassan. In mutum ya kasance a cikina ni kuma a cikinsa, zai ba da’ya’ya da yawa; in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 If anyone does not remain in Me, he is like a branch that is thrown away and withers. Such branches are gathered up, thrown into the fire, and burned.
Duk wanda bai kasance a cikina ba, yana kamar reshen da aka jefar yă bushe; irin waɗannan rassan ne akan tattara, a jefa cikin wuta a ƙone.
7 If you remain in Me and My words remain in you, ask whatever you wish, and it will be done for you.
In kun kasance a cikina kalmomina kuma suka kasance a cikinku, ku roƙi kome da kuke so, za a kuwa ba ku.
8 This is to My Father’s glory, that you bear much fruit, proving yourselves to be My disciples.
Wannan ne yakan kawo ɗaukaka ga Ubana, ku ba da’ya’ya da yawa, kuna kuma nuna kanku ku almajiraina ne.
9 As the Father has loved Me, so have I loved you. Remain in My love.
“Kamar yadda Uba ya ƙaunace ni, haka ni ma na ƙaunace ku. To, fa, ku kasance cikin ƙaunata.
10 If you keep My commandments, you will remain in My love, just as I have kept My Father’s commandments and remain in His love.
In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.
11 I have told you these things so that My joy may be in you and your joy may be complete.
Na gaya muku wannan domin murnata ta kasance a cikinku, murnanku kuma ta zama cikakkiya.
12 This is My commandment, that you love one another as I have loved you.
Umarnina shi ne, Ku ƙaunaci juna kamar yadda na ƙaunace ku.
13 Greater love has no one than this, that he lay down his life for his friends.
Babu ƙaunar da ta fi wannan, a ce mutum ya ba da ransa saboda abokansa.
14 You are My friends if you do what I command you.
Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.
15 No longer do I call you servants, for a servant does not understand what his master is doing. But I have called you friends, because everything I have learned from My Father I have made known to you.
Ba zan ƙara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abin da maigidansa yake yi ba. A maimako in ce da ku abokai, domin na sanar da ku duk abin da na ji daga wurin Ubana.
16 You did not choose Me, but I chose you. And I appointed you to go and bear fruit—fruit that will remain—so that whatever you ask the Father in My name, He will give you.
Ba ku kuka zaɓe ni ba, a’a, ni ne na zaɓe ku na kuma naɗa ku ku je ku ba da’ya’ya-’ya’yan da za su dawwama. Uba kuwa zai ba ku duk abin da kuka roƙa cikin sunana.
17 This is My command to you: Love one another.
Umarnina ke nan. Ku ƙaunaci juna.
18 If the world hates you, understand that it hated Me first.
“In duniya ta ƙi ku, ku san cewa ta fara ƙin na ne.
19 If you were of the world, it would love you as its own. Instead, the world hates you, because you are not of the world, but I have chosen you out of the world.
Da ku na duniya ne, da ta ƙaunaci abinta. Kamar yadda yake, ku ba na duniya ba ne, na zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku.
20 Remember the word that I spoke to you: ‘No servant is greater than his master.’ If they persecuted Me, they will persecute you as well; if they kept My word, they will keep yours as well.
Ku tuna da kalmomin da na yi muku cewa, ‘Ba bawan da ya fi maigidansa,’In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun yi biyayya da koyarwata, da za su yi biyayya da taku ma.
21 But they will treat you like this because of My name, since they do not know the One who sent Me.
Za su yi muku haka saboda sunana, gama ba su san Wannan da ya aiko ni ba.
22 If I had not come and spoken to them, they would not be guilty of sin. Now, however, they have no excuse for their sin.
Da a ce ban zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Yanzu kam, ba su da wata hujja a kan zunubinsu.
23 Whoever hates Me hates My Father as well.
Wanda ya ƙi ni ya ƙi ya ƙi Ubana ma.
24 If I had not done among them the works that no one else did, they would not be guilty of sin; but now they have seen and hated both Me and My Father.
Da a ce ban yi ayyuka a cikinsu waɗanda babu wani da ya taɓa yi ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun ga waɗannan ayyukan banmamaki, duk da haka sun ƙi ni sun kuma ƙi Ubana.
25 But this is to fulfill what is written in their Law: ‘They hated Me without reason.’
Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
26 When the Advocate comes, whom I will send to you from the Father—the Spirit of truth who proceeds from the Father—He will testify about Me.
“Sa’ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, Ruhun gaskiya wanda yake fitowa daga wurin Uba, zai ba da shaida game da ni.
27 And you also must testify, because you have been with Me from the beginning.
Ku ma dole ku ba da shaida, domin kun kasance tare da ni tun daga farko.