< Job 8 >

1 Then Bildad the Shuhite replied:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “How long will you go on saying such things? The words of your mouth are a blustering wind.
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Does God pervert justice? Does the Almighty pervert what is right?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 When your children sinned against Him, He gave them over to their rebellion.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 But if you would earnestly seek God and ask the Almighty for mercy,
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 if you are pure and upright, even now He will rouse Himself on your behalf and restore your righteous estate.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 Though your beginnings were modest, your latter days will flourish.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Please inquire of past generations and consider the discoveries of their fathers.
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 For we were born yesterday and know nothing; our days on earth are but a shadow.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Will they not teach you and tell you, and speak from their understanding?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Does papyrus grow where there is no marsh? Do reeds flourish without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 While the shoots are still uncut, they dry up quicker than grass.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Such is the destiny of all who forget God; so the hope of the godless will perish.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 His confidence is fragile; his security is in a spider’s web.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He leans on his web, but it gives way; he holds fast, but it does not endure.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He is a well-watered plant in the sunshine, spreading its shoots over the garden.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots wrap around the rock heap; he looks for a home among the stones.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 If he is uprooted from his place, it will disown him, saying, ‘I never saw you.’
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Surely this is the joy of his way; yet others will spring from the dust.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Behold, God does not reject the blameless, nor will He strengthen the hand of evildoers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 He will yet fill your mouth with laughter, and your lips with a shout of joy.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Your enemies will be clothed in shame, and the tent of the wicked will be no more.”
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >