< Job 7 >

1 “Is not man consigned to labor on earth? Are not his days like those of a hired hand?
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Like a slave he longs for shade; like a hireling he waits for his wages.
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 So I am allotted months of futility, and nights of misery are appointed me.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 When I lie down I think: ‘When will I get up?’ But the night drags on, and I toss and turn until dawn.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 My flesh is clothed with worms and encrusted with dirt; my skin is cracked and festering.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 My days are swifter than a weaver’s shuttle; they come to an end without hope.
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 Remember that my life is but a breath. My eyes will never again see happiness.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 The eye that beholds me will no longer see me. You will look for me, but I will be no more.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 As a cloud vanishes and is gone, so he who goes down to Sheol does not come back up. (Sheol h7585)
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
10 He never returns to his house; his place remembers him no more.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 Therefore I will not restrain my mouth; I will speak in the anguish of my spirit; I will complain in the bitterness of my soul.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Am I the sea, or the monster of the deep, that You must keep me under guard?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 When I think my bed will comfort me and my couch will ease my complaint,
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 then You frighten me with dreams and terrify me with visions,
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 so that I would prefer strangling and death over my life in this body.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 I loathe my life! I would not live forever. Leave me alone, for my days are but a breath.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 What is man that You should exalt him, that You should set Your heart upon him,
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 that You attend to him every morning, and test him every moment?
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Will You never look away from me, or leave me alone to swallow my spittle?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 If I have sinned, what have I done to You, O watcher of mankind? Why have You made me Your target, so that I am a burden to You?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 Why do You not pardon my transgression and take away my iniquity? For soon I will lie down in the dust; You will seek me, but I will be no more.”
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”

< Job 7 >