< Job 6 >
2 “If only my grief could be weighed and placed with my calamity on the scales.
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 For then it would outweigh the sand of the seas— no wonder my words have been rash.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For the arrows of the Almighty have pierced me; my spirit drinks in their poison; the terrors of God are arrayed against me.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Does a wild donkey bray over fresh grass, or an ox low over its fodder?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Is tasteless food eaten without salt, or is there flavor in the white of an egg?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 My soul refuses to touch them; they are loathsome food to me.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 If only my request were granted and God would fulfill my hope:
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 that God would be willing to crush me, to unleash His hand and cut me off!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 It still brings me comfort, and joy through unrelenting pain, that I have not denied the words of the Holy One.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 What strength do I have, that I should still hope? What is my future, that I should be patient?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Is my strength like that of stone, or my flesh made of bronze?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Is there any help within me now that success is driven from me?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 A despairing man should have the kindness of his friend, even if he forsakes the fear of the Almighty.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 But my brothers are as faithless as wadis, as seasonal streams that overflow,
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 darkened because of the ice and the inflow of melting snow,
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 but ceasing in the dry season and vanishing from their channels in the heat.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 Caravans turn aside from their routes; they go into the wasteland and perish.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 The caravans of Tema look for water; the travelers of Sheba hope to find it.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 They are confounded because they had hoped; their arrival brings disappointment.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 For now you are of no help; you see terror, and you are afraid.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Have I ever said, ‘Give me something; offer me a bribe from your wealth;
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 deliver me from the hand of the enemy; redeem me from the grasp of the ruthless’?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Teach me, and I will be silent. Help me understand how I have erred.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 How painful are honest words! But what does your argument prove?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Do you intend to correct my words, and treat as wind my cry of despair?
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 You would even cast lots for an orphan and barter away your friend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 But now, please look at me. Would I lie to your face?
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Reconsider; do not be unjust. Reconsider, for my righteousness is at stake.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Is there iniquity on my tongue? Can my mouth not discern malice?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?